Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




2 Samaʼila 22:4 - Sabon Rai Don Kowa 2020

4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Littafi Mai Tsarki

4 Na yi kira ga Ubangiji, Ya cece ni daga abokan gābana. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




2 Samaʼila 22:4
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.


Da babbar murya suka rera, “Macancanci ne Ɗan Ragon nan da aka kashe, don yă sami iko da wadata da hikima da ƙarfi da girma da ɗaukaka da kuma yabo!”


gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”


Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.


Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.


Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.


“Ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka cancanci ɗaukaka da girma da iko, domin ka halicci dukan abubuwa, kuma ta wurin nufinka aka halicce su suka kuma kasance.”


Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.


Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.


Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”


Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?


Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!


Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.


Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.


ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”


Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.


Lawiyawan nan, Yeshuwa, Kadmiyel, Bani, Hashabnehiya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya da Fetahahiya, suka ce, “Ku miƙe tsaye ku yabi Ubangiji Allahnku, wanda yake har abada abadin.” “Albarka ta tabbata ga sunanka mai ɗaukaka, bari kuma a ɗaukaka shi bisa dukan albarka da yabo.


Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ