37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
37 Ka hana a kama ni, Ban kuwa taɓa faɗuwa ba.
Sa’ad da kake tafiya, ba abin da zai sa ka tuntuɓe; sa’ad da kake gudu, ba za ka fāɗi ba.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.