19 “Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
19 Ana nan sai ɗan wannan mata ya mutu da dare, domin ta kwanta a kansa.
Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.