20 kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
20 Har wa yau, “Ubangiji ya san tunanin masu hikima banza ne.”
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Ku lura kada wani yă ruɗe ku da ilimin banza da wofi. Wannan koyarwa ta mutane ce kawai. Ta fito daga ikokin wannan duniya ne ba daga Kiristi ba.
Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.