Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zefaniya 2:9 - Littafi Mai Tsarki

9 Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna Allah na Isra'ila, Na rantse cewa, Mowab za ta zama kamar Saduma, Ammonawa kuma za su zama kamar Gwamrata. Za su zama ƙasar ƙayayuwa Da kwazazzaban gishiri marar amfani har abada. Mutanena waɗanda suka ragu za su washe su, su mallake su.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

9 Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zefaniya 2:9
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma, su washe mutanen da suke wajen gabas. Za su ci nasara a kan mutanen Edom da na Mowab, jama'ar Ammon kuwa za su yi musu biyayya.


Dukan ƙasa za ta zama kibritu da gishiri, ba shuka, ba amfani, ciyawa kuma ba ta tsirowa, kamar yadda Ubangiji ya kabantar da Saduma da Gwamrata, da Adam da Zeboyim, da zafin fushinsa.


Ubangiji zai kiyaye Dutsen Sihiyona, amma za a tattake jama'ar Mowab a ƙasa, kamar yadda ake tattake tattaka cikin taki.


Abin da ya faru da Saduma da Gwamrata, Da biranen da suke kewaye da su, Shi ne zai faru da Babila. Ba mutumin da zai zauna cikinta.


Ga abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya faɗa a kan Mowab, “Kaiton Nebo, gama ta lalace! An kunyatar da Kiriyatayim, an ci ta da yaƙi, An kunyatar da kagararta, an rushe ta.


Ki dudduba, ki ɗaga idonki, ki ga abin da yake faruwa! Mutanenki suna tattaruwa suna komowa gida! Hakika, da yake ni ne Allah Mai Rai, Za ki yi fāriya da mutanenki, Kamar yadda amarya take fāriya da kayan adonta!


Domin a rubuce yake, “Na rantse da zatina, in ji Ubangiji, kowace gwiwa sai ta rusuna mini, Kowane harshe kuwa sai ya yabi Allah.”


Waɗanda suka ragu cikin Isra'ila, Ba za su aikata mugunta ba, Ba kuma za su faɗi ƙarya ba, Gama harshen ƙarya ba zai kasance a bakinsu ba. Za su yi kiwo, su kwanta, Ba wanda zai tsorata su.”


Tumaki za su kwanta a tsakiyarta, Da kuma kowace irin dabba ta kowace ƙasa. Mujiya da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta, Ga muryar kuka a taga. Ga risɓewa a bakin ƙofa, Gama za a kware rufin katakan itacen al'ul.


Gaɓar teku za ta zama ta mutanen Yahuza waɗanda suka ragu, Wurin da za su yi kiwo. Za su kwanta da maraice a gidajen Ashkelon, Gama Ubangiji Allahnsu zai kula da su, Zai kuwa mayar musu da albarkarsu ta dā.


Ubangiji ya ce, “Mutanen Ammon sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don haɗamarsu ta ƙasa, Suka tsaga mata masu ciki a Gileyad.


Abin da zai faru ga Edom zai zama daidai da abin da ya faru ga Saduma, da Gwamrata, da biranen da suke kusa da su, a lokacin da aka kaɓantar da su. Ba wanda zai zauna cikinta, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a cikinta, ni Ubangiji na faɗa.


Ni wanda sunana Ubangiji Mai Runduna Sarki ne, Na rantse da raina, wani zai ɓullo, Kamar Tabor a cikin tsaunuka, Ko kuwa kamar Karmel a bakin teku.


Amma, hakika, na rantse da zatina, kamar yadda ɗaukakata za ta cika duniya duka,


Wannan shi ne abin da Ubangiji ya faɗa akan Ammonawa, “Isra'ila ba shi da 'ya'ya ne? Ko kuwa ba shi da māgada ne? Me ya sa waɗanda suke bautar Milkom suka mallaki inda Gad take zama, Suka zauna a garuruwanta?


Hazor za ta zama kufai har abada, wurin zaman diloli, Ba wanda zai zauna a ciki, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a wurin.”


Ubangiji ya ce, “Mutanen Mowab sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun ƙone ƙasusuwan Sarkin Edom Don su yi toka da su.


“Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato 'ya'yan da za su gaje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji zai ɗora mata.


Bari dukan 'yan adam su yi tsit a gaban Ubangiji, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ