Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zakariya 9:7 - Littafi Mai Tsarki

7 Zan kawar da jininsu daga bakinsu, Da kuma haramtattun abubuwa daga haƙoransu. Sauransu za su zama jama'ar Allahnmu, Za su zama kamar sarki cikin Yahuza. Mutanen Ekron za su zama kamar Yebusiyawa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Zan kawar da jini daga bakinsu, zan kuma cire abincin da aka haramta daga tsakanin haƙoransu. Waɗanda za a bari za su zama na Allahnmu, su kuma zama shugabanni a Yahuda, Ekron kuma za tă zama kamar Yebusiyawa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zakariya 9:7
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ba sauran cewa Bayahude ko Ba'al'umme, ko ɗa, ko bawa, ko namiji ko mace. Ai, dukkanku ɗaya kuke, na Almasihu Yesu.


Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, a waɗannan kwanaki mutum goma daga kowace al'umma da kowane harshe za su kama kafa wurin Bayahude, su ce, ‘Ka yardar mana mu tafi tare da kai, gama mun ji Allah yana tare da ku.’ ”


Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci ƙafafu biyu Ko kunne ɗaya na tunkiya daga bakin zaki, Haka nan kuma kima daga cikin mutanen Samariya Waɗanda suke zaman jin daɗi za su tsira.


Amma daga baya zan sa Elam kuma ta wadata. Ni Ubangiji na faɗa.”


“Amma daga baya zan sa Ammonawa su wadata kuma, Ni Ubangiji na faɗa.”


“Amma zan komar da mutanen Mowab nan gaba, Ni Ubangiji na faɗa.” Wannan shi ne hukuncin Mowab.


Ka kakkarya haƙoransu, ya Allah, Ka ciccire fiƙoƙin waɗannan zakoki masu zafin rai, ya Ubangiji!


Ka zo, ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka yi nasara a kan dukan abokan gābana, Ka hallakar da dukan mugaye.


Allah ya aiko mala'ikansa don ya hallaka Urushalima, amma sa'ad da yake gab da hallaka ta, sai Ubangiji ya gani, ya janye shirin annobar, ya ce wa mala'ikan hallakarwa, “Ya isa, janye hannunka.” Mala'ikan Ubangiji kuwa na tsaye kusa da masussukar Arauna Bayebuse.


Tattarmuka za su zauna a Ashdod, Zan kuma sa alfarmar Filistiya ta ƙare.


Zan kafa sansani kewaye da Haikalina saboda maƙiya, Don masu kai da kawowa. Ba wani azzalumi da zai ci su da yaƙi, Gama yanzu ni kaina na gani.”


da Yebusiyawa, da Amoriyawa, da Girgashiyawa,


Da dare sukan tafi cikin kogwanni da kaburbura, suna neman shawarar kurwar matattu. Waɗannan mutane sukan ci naman alade, su kuma sha romon naman da aka miƙa hadaya irin ta arna.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ