Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zakariya 9:17 - Littafi Mai Tsarki

17 Wane irin kyau da bansha'awa alherinsa yake! Hatsi zai sa samari su yi murna. Sabon ruwan inabi kuma zai sa 'yan mata su yi farin ciki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

17 Za su yi kyan gani da kuma bansha’awa! Hatsi zai sa samari su yi murna, sabon ruwan inabi kuma zai sa ’yan mata su yi farin ciki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zakariya 9:17
37 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Wata rana za ku ga sarki mai ɗaukaka yana mulki a dukan ƙasar da take shimfiɗe zuwa kowace kusurwa.


Bakinki kamar ruwan inabi mafi kyau ne. Idan haka ne bari ya bulbulo sosai zuwa ga ƙaunataccena, Ya gangara leɓunan masu barci.


Ƙaunataccena kyakkyawa ne ƙaƙƙarfa kuma, Da ƙyar a sami ɗaya irinsa a cikin dubu goma.


Ka yarda, albarkarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji Allahnmu. Ka sa mu yi nasara game da dukan abin da za mu yi! I, ka ba mu nasara a dukan abin da muke yi!


Allah yana haskakawa daga Sihiyona, Da cikar jamalin Sihiyona.


Kai ne mafi kyau a cikin dukan mutane, Kai mai kyakkyawan lafazi ne, Kullum Allah yakan sa maka albarka!


Ina misalin darajar madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji! Mutane sukan sami mafaka a ƙarƙashin fikafikanka.


Abin al'ajabi ne irin tanadin da ka yi wa masu tsoronka! Abin da kake aikatawa a gaban kowa kuma, Yana da banmamaki. Kana kiyaye waɗanda suke amincewa da kai.


“Ya Ubangiji, wane ne kamarka a cikin alloli? Wa yake kamarka a cikin ɗaukaka da tsarki? Mai banrazana cikin mafifitan ayyuka, mai aikata mu'ujizai.


Shari'a fa, an shigo da ita ne, don laifi yă haɓaka. Amma a inda zunubi ya haɓaka, alherin Allah ma ya fi haɓaka ƙwarai da gaske.


Amma kuwa Allah yana tabbatar mana da ƙaunar da yake yi mana, wato tun muna masu zunubi, Almasihu ya mutu dominmu.


“Saboda ƙaunar da Allah ya yi wa duniya har ya ba da makaɗaicin Ɗansa, domin duk wanda ya gaskata da shi kada ya hallaka, sai dai ya sami rai madawwami.


Kalman nan kuwa ya zama mutum, ya zauna a cikinmu, yana mai matuƙar alheri da gaskiya. Mun kuma dubi ɗaukakarsa, ɗaukaka ce ta makaɗaicin Ɗa daga wurin Ubansa.


“A wannan lokaci tsaunuka za su rufu da kurangar inabi, Tuddai za su cika da shanu, Dukan rafuffukan Yahuza za su gudano da ruwa, Maɓuɓɓuga za ta gudano daga Haikalin Ubangiji, Ta shayar da kwarin Shittim.


Yanzu za ku ci abinci a wadace ku ƙoshi, Za ku yabi sunan Ubangiji Allahnku, Wanda ya yi muku abubuwa masu banmamaki, Ba kuma za a ƙara kunyatar da mutanena ba.


Za su zo su raira waƙa da ƙarfi, A bisa ƙwanƙolin Sihiyona, Za su yi annuri saboda alherin Ubangiji, Saboda hatsi, da ruwan inabi, da mai, Saboda 'ya'yan tumaki da na shanu. Rayuwarsu za ta zama kamar lambu, Ba za su ƙara yin yaushi ba.


Ya Ubangiji, ka dube mu daga Sama, wurin da kake cike da tsarki da ɗaukaka. Ina kulawan nan da kake yi mana? Ina ikon nan naka? Ina ƙaunan nan taka da juyayin nan naka? Kada ka watsar da mu.


Zan faɗi ƙaunar Ubangiji marar ƙarewa, Zan yabe shi saboda dukan abin da ya yi mana. Ya sa wa jama'ar Isra'ila albarka mai yawa, Saboda jinƙansa da ƙaunarsa marar matuƙa.


Za su ba da labarin girmanka duka, Su kuma raira waƙa a kan alherinka.


Ya Ubangiji, kai Allah ne mai jinƙai, mai ƙauna, Mai jinkirin fushi, kullum kai mai alheri ne, mai aminci.


Ya Ubangiji, kai managarci ne, mai yin gafara, Cike kake da madawwamiyar ƙauna ga dukan waɗanda suke yin addu'a gare ka.


Abu guda nake roƙo a wurin Ubangiji, Abu ɗaya kaɗai nake bukata, Shi ne in zauna a masujadar Ubangiji, In yi ta al'ajabin alherinsa Dukan kwanakin raina, In roƙi biyarwarsa a can.


Zan yi wa ran firistoci biki da wadata, Jama'ata za su ƙoshi da alherina, Ni Ubangiji na faɗa.”


Ka sa 'ya'yanmu maza waɗanda suke cikin samartaka, Su zama kamar itatuwan da yake girma da ƙarfi. Ka sa 'ya'yanmu mata Su zama kamar al'amudai, Waɗanda suke adanta kusurwoyin fāda.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ