Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zakariya 14:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Gama zan tattara dukan al'ummai su yi yaƙi da Urushalima. Za a ci birnin, a washe gidajen. Za a yi wa mata faɗe. Za a kai rabin mutanen birnin bauta, amma za a bar sauran mutanen a cikin birnin.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zakariya 14:2
30 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sa'ad da suke cikin halin ƙaƙa naka yi, za a fyaɗa 'ya'yansu ƙasa, su mutu. Za a washe gidajensu, a yi wa matansu faɗe.”


“Sa'ad da kuka ga an kafa mummunan aikin saɓo mai banƙyama a wurin da bai kamata ba (mai karatu fa yă fahimta), to, sai waɗanda suke ƙasar Yahudiya su gudu su shiga duwatsu.


Sarki ya yi fushi, ya tura sojansa, suka hallaka masu kisankan nan, suka ƙone garinsu ƙurmus.


to, ga abin da Ubangiji ya ce maka, ya kai Amaziya, ‘Matarka za ta zama karuwa a birni, za a karkashe 'ya'yanka a cikin yaƙi. Za a rarraba wa waɗansu ƙasarka, kai kanka kuwa za ka mutu a ƙasar arna. Za a sa jama'ar Isra'ila su yi ƙaura zuwa wata ƙasa.’ ”


Zan tattara dukan al'ummai, In kai su kwarin Yehoshafat. A can zan yi musu shari'a A kan dukan abin da suka yi wa jama'ata. Sun warwatsa Isra'ilawa a sauran ƙasashe, Suka rarraba ƙasata.


Ubangiji ya ba da alama a kirawo al'ummar da take nesa. Ya yi musu fīto su zo daga bangon duniya. Ga shi kuwa sun iso da sauri nan da nan.


A kwanakin nan Kaisar Augustas ya yi shela, cewa a rubuta dukkan mutanen da suke ƙarƙashin mulkinsa.


A lokacin nan za a yi wata matsananciyar wahala, irin wadda ba a taɓa yi ba tun farkon halittar da Allah ya yi, har ya zuwa yanzu, ba kuwa za a ƙara yi ba har abada.


Maƙiyi ya miƙa hannunsa A kan dukan kayanta masu daraja, Gama ta ga al'ummai sun shiga Haikali, Su waɗanda ka hana su shiga cikin jama'arka.


Ubangiji ya yi magana da Irmiya sa'ad da Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da dukan sojojinsa, da dukan sojojin mulkokin al'umman da suke a ƙarƙashinsa, da dukan mutane suke yaƙi da Urushalima da dukan biranenta.


Ku yi murna da farin ciki a kan abin da na halitta. Sabuwar Urushalima da nake halittawa za ta cika da murna, jama'arta kuma za su yi farin ciki.


“Ku faɗa wa Zadakiya, Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Ga shi, zan juyo kayan yaƙin da suke hannunka waɗanda kake yaƙi da su gāba da Sarkin Babila, da sojojinsa, waɗanda suka kewaye garun birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.


to, ina gāba da ke, zan hukunta ki a idanun al'ummai.


Ku sanar wa al'ummai da wannan, Su yi shirin yaƙi, Su kira mayaƙa! Su tattaro sojoji, su zo!


“Ga shi, ina gab da sa Urushalima ta zama ƙoƙon sa tangaɗi ga dukan al'ummai da yake kewaye. Yaƙin da zai kewaye Urushalima zai shafi Yahuza ita ma.


A ran nan zan sa Urushalima ta zama dutse mai nauyi ga dukan al'ummai. Duk wanda ya ɗaga ta zai ji wa kansa mugun rauni. Dukan al'umman duniya za su taru su kewaye ta.


A ranar kuma zan hallaka dukan al'umman da suka zo su yi yaƙi da Urushalima.


Duk wanda aka rage a Urushalima, wanda Ubangiji ya nufa da rayuwa, za a ce da shi mai tsarki.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ