Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zakariya 12:3 - Littafi Mai Tsarki

3 A ran nan zan sa Urushalima ta zama dutse mai nauyi ga dukan al'ummai. Duk wanda ya ɗaga ta zai ji wa kansa mugun rauni. Dukan al'umman duniya za su taru su kewaye ta.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zakariya 12:3
31 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje. Amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.”


Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje, amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.”


A wannan rana ba haske. Masu ba da haske za su dushe.


“A ran nan za a buɗe maɓuɓɓuga don wanke zuriyar Dawuda da mazaunan Urushalima daga zunubi da rashin tsarki.


A ran nan za a yi babban makoki a Urushalima kamar mutane suka yi wa Hadadrimmon a filin Magiddo.


su iskoki ne, aljannu masu yin abubuwan al'ajabi, masu zuwa wurin sarakunan duniya duka, don su tara su saboda yaƙi a babbar ranar nan ta Allah Maɗaukaki.


A wannan rana babbar gigicewa daga wurin Ubangiji za ta faɗo musu, har kowa zai kama hannun ɗan'uwansa, ya kai masa dūka.


“A ranan nan zan sa iyalan Yahuza su zama kamar wuta a kurmi, ko kuwa a gonar da hatsi ya nuna. Za su halaka dukan al'umman da suke kewaye da su. Amma mutanen Urushalima za su yi zamansu lami lafiya.


A wannan rana zan firgita kowane doki, in sa mahayinsa ya haukace. Zan lura da mutanen Yahuza, amma zan makantar da dawakan abokan gābansu.


Zan kuma hamɓare gadon sarautan daula, in kuma karya ƙarfin daular al'umman. Zan kuma hallaka karusai da mahayansu. Sojojin dawakai kuma za su kashe junansu da takuba.


Ga shi kuwa, a wannan lokaci Zan hukunta masu zaluntarki, Zan kuma ceci gurgu, Zan tattara korarru, Zan mai da kunyarsu ta zama yabo, Za su yi suna a duniya duka.


Ɓarnar da aka yi wa Lebanon za ta komo kanka, Ka kashe dabbobinta, yanzu dabbobi za su tsorata ka, Saboda jinin mutanen da ka zubar, Da wulakancin da ka yi wa duniya, Da birane, da mazauna a cikinsu.


Da fushi da hasala zan yi sakayya A kan al'umman da ba su yi biyayya ba.”


Ringin Yakubu kuma zai zamar wa al'umman duniya, Kamar yadda zaki yake a tsakanin namomin jeji, Kamar kuma yadda zaki yake a tsakanin garkunan tumaki, Wanda, sa'ad da ya ratsa, yakan tattaka, Ya yi kacakaca da su, Ba wanda zai cece su.


Jama'ar Yakubu za ta zama kamar wuta, Jama'ar Yusufu kuwa kamar harshen wuta, Jama'ar Isuwa za ta zama kamar tattaka. Za su ƙone ta, su ci ta, ba wanda zai tsira. Ni Ubangiji na faɗa.”


Amma al'umman da ba su bauta miki ba, Za a hallakar da su.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ