Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zakariya 11:8 - Littafi Mai Tsarki

8 A wata guda na hallaka makiyayan nan uku, gama ban jure da su ba, su ma sun gaji da ni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Cikin wata guda na kawar da makiyayan nan uku. Garken suka ƙi ni, na kuwa gaji da su

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zakariya 11:8
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

In duniya ta ƙi ku, ku sani sai da ta ƙi ni kafin ta ƙi ku.


Ba dama duniya ta ƙi ku, amma ni take ƙi, don na shaide ta a kan ayyukanta mugaye ne.


Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Mai Fansa, Ya ce wa wanda aka raina ƙwarai, Al'ummai suka ƙi shi, Bawa na masu mulki kuma, “Sarakuna za su gan ka a sake, Su kuma miƙe tsaye su ba ka girma, Shugabanni su kuma za su gani, Su rusuna har ƙasa su ba ka girma.” Wannan kuwa zai faru saboda Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ya zaɓi bawansa, Ya kuwa cika alkawaransa.


Amma mutanensa suka ƙi shi, har suka aiki jakadu a bayansa, cewa ba sa so ya yi mulki a kansu.


Sun ci amanar Ubangiji. Su haifi shegu. Yanzu amaryar wata za ta cinye su da gonakinsu.”


Amma adalina, ta wurin bangaskiya zai rayu. Amma in ya ja da baya, ba zan yi farin ciki da shi ba.”


Ubangiji ya ce, “Kowace irin muguntarsu tana a Gilgal, A can na ƙi su! Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga ƙasata, Ba kuma zan ƙaunace su ba. Dukan shugabanninsu 'yan tayarwa ne.


Saboda darajar sunanka, kada ka wulakanta mu, Kada kuma ka ƙasƙantar da darajar kursiyinka, Ka tuna da alkawarin da ka yi mana, Kada ka ta da shi.


Abin gādona ya zama mini kamar zaki a cikin kurmi, Ya ta da murya gāba da ni, Domin haka na ƙi shi.


Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da jama'arsa, Ransa bai ji daɗinsu ba.


“Ubangiji ya gani, ya raina su, Saboda tsokanar da 'ya'yansa mata da maza suka yi masa.


Duk da haka, sa'ad da suke a ƙasar maƙiyansu ba zan wulakanta su ba, ba kuwa zan ji ƙyamarsu, har da zan karya alkawarina da su ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu.


Zan lalatar da masujadanku, in rurrushe bagaden ƙona turarenku, in jefar da gawawwakinku a kan gumakanku, raina kuwa zai ji ƙyamarku.


Zan kafa wurin zamana a tsakiyarku, ba kuwa zan gaji da ku ba.


Ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa ɗokanta ƙwarai har a yi mini ita!


Ifraimawa waɗanda suka yi yaƙi da bakkuna da kibau Suka gudu a ranar yaƙi.


Ba ka jurewa da ganin mutane masu fāriya, Kana ƙin mugaye.


Ana ce da su ƙwan maƙerar azurfa ne, Gama ni na ƙi su.”


domin in kama zukatan mutanen Isra'ila waɗanda suka zama baƙi a gare ni, saboda gumakansu.


Ke 'yar mahaifiyarki ce wadda ta ƙi mijinta da 'ya'yanta. Ke kuma 'yar'uwar 'yar'uwanki mata ce waɗanda suka ƙi mazansu da 'ya'yansu. Mahaifiyarki Bahittiya ce, mahaifinki kuwa Ba'amore ne.


Mutanena sun lalace saboda jahilci. Tun da yake sun ƙi ilimi, Ni ma na ƙi ku da zaman firist ɗina. Tun da yake kun manta da umarnan Allahnka, Ni ma zan manta da 'ya'yanku.


Ya zama abokin gāban Isra'ila a dukan zamanin Sulemanu. Ya yi ta ɓarna kamar yadda Hadad ya yi. Ya ƙi jinin mutane Isra'ila. Ya yi mulkin suriya.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ