Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zakariya 11:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ki buɗe ƙofofinki, ke Lebanon, Don wuta ta cinye itatuwan al'ul naki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Buɗe ƙofofinki, ya Lebanon, don wuta ta cinye itatuwan al’ul naki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zakariya 11:1
14 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya ku mazaunan Lebanon, Waɗanda suke zaune cikin itatuwan al'ul, Irin nishin da za ku yi sa'ad da azaba ta same ku, Azaba ce irin ta mace mai naƙuda!


Zan dawo da su gida daga ƙasar Masar, In tattaro su daga Assuriya, Zan kawo su a ƙasar Gileyad da ta Lebanon, Har su cika, ba sauran wuri.


Ku haura zuwa kan tuddai, ku kawo itace don ku gina Haikalina, in ji daɗinsa, a kuma ɗaukaka ni.


Ɓarnar da aka yi wa Lebanon za ta komo kanka, Ka kashe dabbobinta, yanzu dabbobi za su tsorata ka, Saboda jinin mutanen da ka zubar, Da wulakancin da ka yi wa duniya, Da birane, da mazauna a cikinsu.


Saboda ka washe al'umman duniya da yawa, Sauran mutanen duniya duka za su washe ka, Saboda jinin mutane, da wulakancin da ka yi wa duniya, Da birane, da mazauna a cikinsu.


Gama fushina ya kama wuta, Tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za ta cinye duniya da dukan amfaninta, Za ta kama tussan duwatsu.


Kana kama da Assuriya mai kama da itacen al'ul a Lebanon, Mai rassa masu kyau da inuwar kurmi, Mai tsayi ainun, kansa ya kai cikin gizagizai.


Ka yi kuka, kai itacen kasharina, Gama itacen al'ul ya riga ya fāɗi, Itatuwa masu daraja sun lalace, Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan, Saboda an sassare itatuwan babban kurmi.


“A ranan nan zan sa iyalan Yahuza su zama kamar wuta a kurmi, ko kuwa a gonar da hatsi ya nuna. Za su halaka dukan al'umman da suke kewaye da su. Amma mutanen Urushalima za su yi zamansu lami lafiya.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ