Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 8:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Sa'ad da na duba sararin sama, wanda ka yi, Da wata da taurari waɗanda ka sa a wuraren zamansu,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Sa’ad da na dubi sammai, aikin yatsotsinka, wata da taurari waɗanda ka ajiye a wurarensu,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 8:3
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

A sa'ad da Allah ya fara halittar Sama da duniya,


Ubangiji ya halicci duniya da umarninsa, Rana, da wata, da taurari kuma bisa ga maganarsa.


Abubuwan banmamaki ne Ubangiji yake aikatawa! Duk waɗanda suke murna da su Suna so su fahimce su.


Ka halicci wata don ƙididdigar lokatai, Rana kuwa ta san daidai lokacin fāɗuwarta.


Duniya taka ce, haka ma samaniya taka ce, Kai ne ka halicci duniya da dukan abin da yake cikinta.


Gama tun daga halittar duniya al'amuran Allah marasa gănuwa, wato ikonsa madawwami, da allahntakarsa, sun fahimtu sarai, ta hanyar abubuwan da aka halitta kuma ake gane su. Saboda haka mutane sun rasa hanzari.


Ni kuwa in da ikon Allah nake fitar da aljannu, ashe, Mulkin Allah ya zo muku ke nan.


Sai masu sihiri suka ce wa Fir'auna, “Ai, wannan aikin Allah ne.” Amma zuciyar Fir'auna ta taurare, har da bai kasa kunne ga Musa da Haruna ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.


“Ashe, ba a can saman sammai Allah yake zaune ba? Sai ya sunkuya ya dubi taurari, ko da yake suna can sama ne.


Ku lura fa, sa'ad da kuka dubi sama, kuka ga rana, da wata, da taurari, da dai dukan rundunar sama, don kada fa ku jarabtu, ku yi musu sujada, ko ku bauta musu. Ubangiji Allahnku ya sa waɗannan saboda dukan al'ummai.


Sa'ad da ya gama magana da Musa a kan Dutsen Sina'i, sai ya ba shi alluna biyu na shaida, allunan duwatsu rubatattu da yatsan Allah.


Ku yabe shi, ku rana da wata, Ku yabe shi, ku taurari masu haskakawa!


Dubi yadda sararin sama yake bayyana ɗaukakar Allah! Dubi yadda suke bayyana a fili ayyukansa da ya yi!


Hasken wata ba haske ba ne a gare shi, Ko taurari ma ba su da tsarki a gabansa.


Akwai wanda zai iya ƙidaya mala'ikun da suke masa hidima? Akwai wurin da hasken Allah bai haskaka ba?


“Ka tuna ka girmama aikinsa, Wanda mutane suke yabo.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ