Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 8:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ya Ubangiji, Ubangijinmu, An san girmanka ko'ina a dukan duniya. Yabonka ya kai har sammai,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ya Ubangiji, shugabanmu, sunanka da girma take a cikin dukan duniya! Ka kafa ɗaukakarka bisa sammai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 8:1
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya Ubangiji, Ubangijinmu, An san girmanka ko'ina a dukan duniya!


Bari dukansu su yabi sunan Ubangiji, Sunansa ya fi dukan sauran sunaye girma, Ɗaukakarsa kuwa tana bisa duniya da samaniya!


Ka bayyana girmanka ya Allah, a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!


“Ya Ubangiji, wane ne kamarka a cikin alloli? Wa yake kamarka a cikin ɗaukaka da tsarki? Mai banrazana cikin mafifitan ayyuka, mai aikata mu'ujizai.


Daga Edom Allah ya zo, Daga dutsen Faran Mai Tsarki yake tahowa. Ɗaukakarsa ta rufe sammai, Duniya kuwa ta cika da yabonsa.


Zan yi shelar girmanka, ya Allahna, Sarkina, Zan yi maka godiya har abada abadin.


Irin babban firist wanda muke bukata ke nan, mai tsarki, marar aibu, marar cikas, keɓaɓɓe daga masu zunubi, ɗaukakke kuma birbishin sammai.


Ya Ubangiji Allahnmu, waɗansu sun mallake mu, Amma kai kaɗai ne Ubangijinmu.


Sai na ji kamar wata sowar ƙasaitaccen taro, kamar ƙugin ruwa mai gudu, kamar aradu mai ƙara, suna cewa, “Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu Maɗaukaki shi ne yake mulki.


Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah Mai Cetonmu, Ku raira yabbai ga Allah na Yakubu!


Madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji, Ta kai har sammai, Amincinka ya kai sararin sammai.


“Idan ba ku lura, ku aikata dukan maganar dokokin nan da aka rubuta a wannan littafi ba, domin ku ji tsoron sunan nan mai ɗaukaka, mai kwarjini, wato sunan Ubangiji Allahnku,


Dahir na ɗauki dukkan abubuwa hasara ne, a kan mafificiyar darajar sanin da nake yi na Almasihu Yesu Ubangijina. Saboda shi ne na zaɓi yin hasarar dukkan abubuwa, har ma na mai da su tozari domin Almasihu yă zama nawa,


Ina ƙaunar Haikalinka ƙwarai, Ya Allah Mai Iko Dukka!


Ku raira waƙa ga Allah, Ku raira waƙar yabo ga sunansa, Ku yi hanya ga wanda yake ratsa gizagizai. Sunansa kuwa Ubangiji ne, ku yi murna a gabansa!


Ya Allah, kai ne Allahna, Ina sa zuciya gare ka. Duk niyyata ta nemanka ce, Raina yana ƙishinka, Kamar bussasshiyar ƙasa, Wadda ta zozaye, ba ta da ruwa.


“Amma ko Allah zai zauna a duniya? Ga shi, Saman sammai ba ta isa ta karɓe ka ba, balle wannan Haikali da na gina!


Shi wanda ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau a can birbishin dukkan sammai, domin yă cika kome.)


Bakinsa yana da daɗin sumbata, Kome nasa yana faranta mini rai. Matan Urushalima, yadda ƙaunataccena yake ke nan.


Toma ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangijina Allahna kuma!”


“Tun da Dawuda ya kira shi Ubangiji ne, to, ƙaƙa zai zama ɗansa?”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ