Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 7:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ya Ubangiji, Allahna, na sami mafaka a wurinka, Ka cece ni, ka tserar da ni daga dukan masu fafarata,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 7:1
29 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kana lura da ni kullum, Ka cece ni daga magabtana, Daga waɗanda suke tsananta mini.


Addu'ar nasara wadda annabi Habakuk ya yi.


Saboda haka, sai duk masu shan wuya bisa ga nufin Allah su danƙa ransu ga Mahalicci mai aminci suna aikata abin da yake daidai.


Za ku gudu zuwa kwarin duwatsuna, gama kwarin duwatsu zai kai har Azel, kamar yadda kakanninku suka gudu a zamanin Azariya, Sarkin Yahuza, a lokacin da aka yi girgizar ƙasa. Sa'an nan Ubangiji Allahna zai zo tare da dukan tsarkakansa!


Na yi addu'a ga Ubangiji Allahna, na tuba. Na ce, “Ya Ubangiji, Allah maigirma, mai banrazana, kai mai cika alkawari ne, kana ƙaunar masu ƙaunarka waɗanda suke kiyaye dokokinka.


“Na ji Ifraimu yana baƙin ciki, yana cewa, ‘Ka hore ni, na kuwa horu, Kamar ɗan maraƙin da ba shi da horo, Ka komo da ni don in zama kamar yadda nake a dā, Gama kai ne Ubangiji Allahna.


Amma Ubangiji kana tare da ni Kamar jarumi mai bantsoro, Don haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe, Ba za su rinjaye ni ba. Za su sha kunya ƙwarai, Gama ba za su yi nasara ba. Ba za a manta da su ba.


Sa'an nan Irmiya ya ce, “Ya Ubangiji, ka sani. Kai ne, ka ziyarce ni, Ka kuma sāka wa waɗanda suke tsananta mini. Ka sani saboda kai nake shan zargi.


Ku duka da kuke tsoron Ubangiji, Kuna kuma biyayya da kalmomin bawansa, Zai yiwu hanyar da kuke bi ta yi duhu ƙwarai, Amma ku dogara ga Ubangiji, ku jingina ga Allahnku.


Zai ce mini, ‘Kai ubana ne da Allahna, Kai ne kake kiyaye ni, kai ne Mai Cetona.’


Sa'an nan zan tafi wurin bagadenka, ya Allah, Zuwa gare ka, kai wanda kake sa ni in yi murna da farin ciki, In raira waƙar yabo a gare ka da garayata, Ya Allah, Allahna!


Tilas ne mugu yă sha wahala, Amma masu dogara ga Ubangiji, Madawwamiyar ƙaunarsa tana kiyaye su.


Don haka ba zan yi shiru ba, Zan raira maka yabo, Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan gode maka har abada.


Na roƙi taimako a gare ka, ya Ubangiji Allahna, Ka kuwa warƙar da ni.


Ka hurta rashin laifina, ya Ubangiji, Gama na yi abin da suke daidai, Na dogara gare ka gaba ɗaya.


Ubangiji yakan ba ni haske, Allah yakan kawar da duhuna.


Ubangiji ne Mai Cetona, Shi ne garkuwata mai ƙarfi. Allahna, shi ne yake kiyaye ni, Lafiya nake sa'ad da nake tare da shi, Yana kiyaye ni kamar garkuwa, Yana kāre ni, ya ba ni lafiya.


Amma ina dogara ga madawwamiyar ƙaunarka, Zan yi murna gama za ka cece ni.


Ka dube ni, ya Ubangiji Allahna, ka amsa mini, Ka mayar mini da ƙarfina, don kada in mutu.


Na dogara ga Ubangiji domin zaman lafiya, Wauta ce idan kun ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu,


Ka zo, ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka yi nasara a kan dukan abokan gābana, Ka hallakar da dukan mugaye.


Amma 'yan'uwana da muka tafi tare, sun karya zukatan jama'ar, amma ni na bi Ubangiji Allahna da aminci.


To gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya ta da shi daga matattu, ya kuma ɗaukaka shi, domin bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.


A gare ka nake dogara, ya Allah. Ka cece ni daga shan kunyar fāɗuwa, Kada ka bar magabtana su yi mini duban wulakanci!


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ