Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 69:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Kamar baƙo nake ga 'yan'uwana, Haka ma ga iyalina, kamar baƙo nake.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Ni baƙo ne a cikin ’yan’uwana, bare kuma ga ’ya’yan mahaifiyata maza;

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 69:8
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Magabtana duka suna mini ba'a, Maƙwabtana sun raina ni, Waɗanda suka san ni kuwa suna jin tsorona, Sa'ad da suka gan ni a kan titi sukan guje mini.


Ya zo ga abin mulkinsa ne, jama'a tasa kuwa ba ta karɓe shi ba.


Domin ko dā ma 'yan'uwansa ba su gaskata da shi ba.


Abokaina da maƙwabtana ba su ko zuwa kusa da ni, saboda miyakuna, Har iyalina ma sun guje mini.


Muka raina shi, muka ƙi shi, Ya daure da wahala da raɗaɗi. Ba wanda ya ko dube shi. Muka yi banza da shi kamar shi ba kome ba ne.


Lokacin da Dawuda yake magana da mutanen, sai Eliyab babban wansa ya ji, ya husata, ya ce wa Dawuda, “Me ya kawo ka nan? Wa ka bar wa 'yan tumakin nan a jeji? Na san rigimarka da taurinkanka, ka zo ne don ka yi kallon yaƙi.”


Amma duk wannan ya auku ne domin a cika littattafan annabawa.” Daga nan duk almajiran suka yashe shi, suka yi ta kansu.


Ya Ubangiji, kada ka manta da yadda maƙiyanka suka ci mutuncin zaɓaɓɓen sarki da ka naɗa! Suka yi ta cin mutuncinsa duk inda ya tafi.


Na tsiraita ga masu dūkana. Ban hana su sa'ad da suke zagina ba, Suna tsittsige gemuna, Suna tofa yau a fuskata.


Amma ya daure da wahala wadda a ainihi tamu ce, Raɗaɗin da ya kamata mu ne za mu sha shi. Mu kuwa muna tsammani wahalarsa Hukunci ne Allah yake yi masa.


Sa'an nan Irmiya ya ce, “Ya Ubangiji, ka sani. Kai ne, ka ziyarce ni, Ka kuma sāka wa waɗanda suke tsananta mini. Ka sani saboda kai nake shan zargi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ