Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 69:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Na gaji da kira, ina neman taimako, Maƙogwarona yana yi mini ciwo, Idanuna duka sun gaji, Saboda ina zuba ido ga taimakonka.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 69:3
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Na gaji tiƙis saboda baƙin ciki, Kowane dare gadona yakan jiƙe saboda kukana. Matashin kaina ya yi sharkaf da hawaye.


Muryata ƙarama ce, ba kuma ƙarfi, Na kuwa yi kuka kamar kurciya, Idanuna sun gaji saboda duban sama. Ya Ubangiji, ka cece ni daga dukan wannan wahala.


Idanuna sun gaji da duban hanyar cetonka, Ceton da ka alkawarta.


Idanuna sun gaji da zuba ido ga alkawarinka. Roƙo nake, “Sai yaushe za ka taimake ni?”


A idonku za a ba da 'ya'yanku mata da maza ga wata al'umma dabam, za ku yi ta jin kewarsu, amma a banza, gama ba ku da ikon yin kome.


Almasihu, a lokacin zamansa a duniya, ya yi addu'o'i da roƙe-roƙe, tare da kuka mai tsanani, har da hawaye, ga wannan da yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa saurare shi saboda tsananin miƙa kansa.


Bayan haka, Yesu da ya san duk an gama kome, domin a cika Nassi sai ya ce, “Ina jin ƙishirwa.”


Idanuna sun dushe saboda kuka, Raina yana cikin damuwa. Zuciyata ta karai saboda halakar mutanena, Gama 'yan yara da masu shan mama Sun suma a titunan birnin.


Sa'ad da na ji yunwa, sai suka ba ni dafi, Sa'ad da na ji ƙishi, sai suka ba ni ruwan tsami.


“A kan me zan sa zuciya, ya Ubangiji? A gare ka nake dogara.


Ka sa nagartata da amincina su kiyaye ni, Gama na dogara gare ka.


Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura, Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama. Ka bar ni matacce cikin ƙura.


Da rana na yi kira a gare ka, ya Allahna, Amma ba ka amsa ba. Da dare kuma na yi kira, Duk da haka ban sami hutawa ba.


Na yi ta kuka har fuskata ta zama ja wur, Idanuna kuma suka yi luhuluhu.


Amma mugaye za su dudduba ko'ina da fid da zuciya, Ba su da wata hanyar da za su kuɓuta. Sauraronsu kaɗai shi ne mutuwa.”


Ya koya mini raira sabuwar waƙa, Waƙar yabon Allahnmu. Da yawa idan suka ga wannan za su tsorata, Za su kuwa dogara ga Ubangiji.


Fushinka yana da nauyi a kaina, An turmushe ni a cikin tuƙuƙinka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ