Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 68:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Ku raira waƙa ga Allah, Ku raira waƙar yabo ga sunansa, Ku yi hanya ga wanda yake ratsa gizagizai. Sunansa kuwa Ubangiji ne, ku yi murna a gabansa!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 68:4
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Babu wani kamar Allahn Yeshurun, Wanda yakan sauko daga Sama don ya cece ka, Wanda ya sauko daga bisa da ɗaukakarsa.


Duk wanda yake a duniya, yana yi maka sujada, Yana raira maka waƙar yabbai, Yana raira yabbai ga sunanka.”


Ka gina wurin zamanka a bisa kan ruwan da yake sama. Gajimare ne karusanka, A bisa kan fikafikan iska kake tafiya.


Shi wanda ya hau cikin sararin sama, Daɗaɗɗen sararin sama! Ku kasa kunne ga muryarsa mai ƙarfi!


Ku raira waƙar darajar sunansa, Ku yabe shi da ɗaukaka!


Da ma sauran al'umma su yi murna, su raira waƙa ta farin ciki, Domin kana yi wa jama'a shari'a ta adalci, Kana kuma bi da dukan sauran al'umma.


Ya sauko ta bisa bayan kerubobi, Yana tafe da sauri a kan fikafikan iska.


Murya tana kira tana cewa, “Ka shirya hanya a jeji domin Ubangiji! Ka share hanya a hamada domin Allahnmu!


Ka sa su sani kai kaɗai ne Ubangiji, Kai kaɗai ne mamallakin dukan duniya!


Sa'an nan zan kawo ku cikin ƙasar da na rantse zan bai wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. Zan ba ku ita ta zama mallakarku. Ni ne Ubangiji.’ ”


Na bayyana ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu a kan ni Allah Maɗaukaki ne, amma sunan nan nawa, Yahweh, ban sanasshe su ba.


Allah kuwa ya ce wa Musa, “NI INA NAN YADDA NAKE,” ya kuma ce, “Haka za ka faɗa wa Isra'ilawa, ‘NI NE ya aiko ni gare ku.’ ”


Ku mutanen Urushalima, ku fita daga cikin birni, Ku gyara hanyoyi domin jama'arku da suke komowa! Ku shirya babbar hanya, Ku kawar da duwatsu daga hanyar! Ku sa alama domin al'ummai su sani,


Wannan shi ne jawabi a kan Masar. Ubangiji yana zuwa Masar a kan girjije a sukwane. Gumakan Masarawa za su yi rawar jiki a gabansa, zuciyar Masarawa za ta karai.


Ka sa wa masu yi maka biyayya albarka, ya Ubangiji, Alherinka yana kāre su kamar gārkuwa.


Za ka nuna mini hanyar rai, Kasancewarka takan sa in cika da farin ciki, Taimakonka kuwa yana kawo jin daɗi har abada.


Haske yakan haskaka adalai, Haka kuma murna ta cika ga masu nagarta.


Abin da mutanen kirki suke sa zuciya yakan kai su ga murna, amma mugaye ba su da wani abu da za su sa zuciya a kai.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ