Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 68:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Kamar yadda iska take korar hayaƙi, Haka nan zai kore su, Kamar yadda kākin zuma yakan narke a gaban wuta, Haka nan mugaye za su hallaka a gaban Allah.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 68:2
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Duwatsu za su narke a ƙarƙashinsa, Kwaruruka za su tsattsage kamar kakin zuma a gaban wuta, Kamar ruwa yana gangarowa daga tsauni.


Amma mugaye za su mutu, Magabtan Ubangiji kuwa za su shuɗe kamar furen jeji, Za su ɓace kamar hayaƙi.


Don haka za su zama kamar ƙāsashin da akan yi da safe, Ko kuwa kamar raɓa mai kakkaɓewa da wuri. Za su zama kamar ƙaiƙayi wanda ake shiƙarsa cikin iska a masussuka, Ko kuwa kamar hayaƙin da yake fita ta bututu.


Muguntar jama'a tana ci kamar wutar da take cinye ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya. Tana ci kamar wutar dawa wadda hayaƙinta take murtukewa har sama.


Tuddai sun narke a gaban Ubangiji kamar kākin zuma, A gaban Ubangijin dukan duniya.


Abokan gābanmu sun sa mata wuta, sun sare ta, Ka yi fushi da su, ka hallaka su!


Za su karkaɗu kamar ruwan da yake tafasa a wuta. Ka zo ka bayyana ikonka a kan abokan gābanka, ka sa al'ummai su yi rawar jiki a gabanka.


Amma mutane suna jin tsoronka! Wa zai iya tsayawa a gabanka Sa'ad da ka yi fushi?


Ƙarfina ya ƙare, Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa. Dukan gaɓoɓina sun guggulle, Zuciyata ta narke kamar narkakken kakin zuma.


Duk kuma lokacin da akwatin zai tashi, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji, ka sa maƙiyanka su warwatse, ka sa waɗanda suke ƙinka su gudu gabanka.”


Sa'an nan Yowab da mutanensa suka matsa, su gabza da Suriyawa. Suriyawa kuwa suka gudu.


Amma Suriyawa suka gudu daga gaban Isra'ilawa. Dawuda kuwa ya kashe Suriyawa, mahayan karusai ɗari bakwai, da mahayan dawakai dubu arba'in (40,000). Aka yi wa Shobak shugaban rundunarsu rauni wanda ya zama ajalinsa, a can ya rasu.


Lokacin da kake yaƙi dominmu, al'ummai sukan gudu daga bakin dāga.


Me ya sa gunkinka, Afis, ya fāɗi, Wato bijimi, gunkinka bai tsaya ba? Domin Ubangiji ya tunkuɗe shi ƙasa!


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ