Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 6:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Ka ji tausayina, gama na gaji tiƙis, Ka wartsarkar da ni, gama na tafke sarai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 6:2
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Mutane sun ce, “Zo, mu koma wurin Ubangiji, Gama shi ne ya yayyaga, Shi ne kuma zai warkar. Shi ne ya yi mana rauni, Shi ne kuma zai ɗaure raunin da maɗauri.


Baƙin ciki ya gajerta kwanakina, Kuka kuma ya rage shekaruna. Na raunana saboda yawan wahalata, Har ƙasusuwana suna zozayewa!


Na roƙi taimako a gare ka, ya Ubangiji Allahna, Ka kuwa warƙar da ni.


Ubangiji, ka warkar da ni, zan kuwa warke, Ka cece ni, zan kuwa cetu, Gama kai ne abin yabona.


Bari in ji sowa ta farin ciki da murna. Ko da yake ka ragargaza ni, Ka kakkarya ni, duk da haka zan sāke yin murna.


“ ‘Ku duba fa, ni ne shi, Ba wani Allah, banda ni, Nakan kashe, in rayar, Nakan sa rauni, nakan kuma warkar, Ba wanda zai cece su daga hannuna.


Ina fama da zazzaɓi, Ina rashin lafiya ƙwarai.


Saboda fushinka ina ciwo mai tsanani, Duk jikina ya kamu da ciwo saboda zunubina.


Sa'ad da ban hurta zunubaina ba, Na gajiyar da kaina da yawan kuka dukan yini.


Ibrahim ya yi addu'a ga Allah, Allah kuwa ya warkar da Abimelek, da matarsa, da bayinsa mata, har kuma suka sami haihuwa.


Ta haka ya shahara a cikin duk ƙasar Suriya. Aka kuwa kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farraɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su.


Ƙarfina ya ƙare, Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa. Dukan gaɓoɓina sun guggulle, Zuciyata ta narke kamar narkakken kakin zuma.


Allah yakan yi maganin raunin da ya yi maka, Ciwon da ya ji maka da hannunsa, Da hannunsa yakan warkar.


Sai Musa ya roƙi Ubangiji, ya ce, “Ina roƙonka, ya Allah, ka warkar da ita.”


Ya ce, “In za ku himmantu ku yi biyayya da ni, ni da nake Ubangiji Allahnku, sai ku aikata abin da yake daidai a gare ni, ku kuma kiyaye umarnaina da dokokina duka, to, ba zan sa muku cuce-cuce irin waɗanda na sa wa Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”


Ku abokaina ne! Ku ji tausayina! Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa.


Ka hukunta ni, ka kuwa yi mini rauni, Ka kuma buge ni har ƙasa.


Ka tsauta mini, ya Ubangiji, amma da adalcinka, Ba da fushinka ba, don kada ka wofinta ni.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ