Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 53:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah.” Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al'amura, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Wawa ne kawai yakan ce a zuciyarsa, “Ba Allah.” Sun lalace, kuma hanyoyinsu ba su da kyau; babu wani mai aikata abu mai kyau.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 53:1
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Mugun mutum da girmankansa yana cewa, “Ba Allah!” Wannan ne abin da mugu yake tunani.


Tun da yake sun ƙi su yarda su san Allah, Allah ya sallama su ga halin banza, su aikata abin kunya.


Amma Allah ya ce masa, ‘Kai marar azanci! A daren nan za a karɓi ranka. To, kayan da ka tanada, na wa za su zama?’


Mutum yakan sha mugunta kamar yadda yake shan ruwa, Hakika mutum ya lalace, ya zama mai rainako.


Fiye da haka kuma akwai mata da maza da suke aikin karuwanci a wuraren da suke tsafin a wurin al'ummai. Mutanen Yahuza sun yi dukan abubuwan ƙazanta na al'ummai waɗanda Ubangiji ya kora sa'ad da Isra'ilawa suke gab da shigar ƙasar.


Lalle zaman da kuka yi na dā, irin wanda al'ummai suke son yi, ya isa haka nan, wato zaman fajirci, da mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa, da shashanci, da shaye-shaye, da kuma bautar gumaka, abar ƙyama.


Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da suke yi a asirce.


Amma ni ina gaya muku, kowa yake fushi da ɗan'uwansa ma, za a hukunta shi. Kowa ya ce da ɗan'uwansa wawa, za a kai shi gaban majalisa. Kowa kuma ya ce, ‘Kai wofi!’ hakkinsa shiga Gidan Wuta.


Yaya mugun zai riƙa raina Allah, Har yă riƙa ce wa kansa, “Ba zai hukunta ni ba”?


Mugun mutum yakan ce wa kansa, “Allah bai kula ba! Ya rufe idonsa, ba zai taɓa ganina ba.”


Yana ce wa kansa “Ba zan taɓa fāɗuwa ba, Ba zan taɓa shan wahala ba.”


Ba wani abu tsarkakakke Da zai fito daga cikin kowane marar tsarki, kamar mutum.


Yerobowam kuwa ya ce a zuciyarsa, “Mulkin fa zai koma gidan Dawuda.


Kada ku yi wa Ubangiji Allahnku haka, gama sun yi wa gumakansu dukan abar ƙyamar da Ubangiji yake ƙi, har sun ƙona wa gumakansu 'ya'yansu mata da maza.


Domin kuwa ko da yake sun san da Allah, duk da haka ba su ɗaukaka shi a kan shi Allah ne ba, ba su kuma gode masa ba. Sai tunaninsu ya wofince, zuciyarsu marar fahimta kuma ta duhunta.


“Samariya ba ta aikata rabin zunubin da kika aikata ba. Abubuwan banƙyama da kika aikata sun sa 'yan'uwanki sun zama kamar adalai.


Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.


Ga wani abin da wawa ba zai iya sani ba, Dakiki kuma ba zai iya ganewa ba,


Ya Ubangiji Allah, Mai Cetona, Duk yini ina ta kuka, Da dare kuma na zo gare ka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ