Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 51:16 - Littafi Mai Tsarki

16 Ba ka son sadakoki, ai, da na ba ka, Ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 51:16
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ba ka bukatar baye-baye da hadayu, Ba ka so a miƙa maka hadayun ƙonawa Na dabbobi a bisa bagade ba, Ko baya-baye don a kawar da zunubai. A maimakon haka, ka ba ni kunnuwan da zan saurare ka.


Gama ƙauna nake so, ba sadaka ba, Sanin Allah kuma fiye da hadayu na ƙonawa.


Sai Sama'ila ya ce, “Me Ubangiji ya fi so? Biyayya, ko kuwa sadakoki da hadayu? Ya fi kyau a yi masa biyayya, da a miƙa masa hadayar tumaki mafi kyau.


Amintacciyar zuciya ita kake so, Ka cika tunanina da hikimarka.


Ubangiji yana ƙin hadayar da mugaye suka miƙa masa, tun ba wadda suka miƙa ta da mugun nufi ba.


Ubangiji yana murna sa'ad da adalai suke yin addu'a, amma yana ƙin hadayun da mugaye suke miƙa masa.


Ban tsauta muku saboda hadayunku ba, Ko saboda hadayu na ƙonawa da kuke ta miƙa mini kullum.


“Saboda haka za ka faɗa musu waɗannan abubuwa duka, amma ba za su ji ka ba. Za ka kira su, amma ba za su amsa ba.


“Idan aka iske wani yana kwance da matar wani, sai a kashe dukansu biyu, wato mutumin da matar. Haka za ku kawar da mugunta daga Isra'ila.


Idan bisa ga kuskure wani mutum ya yi zunubi, sai ya ba da 'yar akuya bana ɗaya ta yin hadaya don zunubi.


Amma idan mutum ya fāɗa wa ɗan'uwansa da niyyar kisankai, lalle, sai a kashe shi ko da ya gudu zuwa bagadena.


Kada ku karɓi fansa don ran wanda ya yi kisankai, dole ne a kashe shi.


Me ya sa ka raina maganar Ubangiji, har da ka aikata mugun abu haka a gabansa? Ka kashe Uriya Bahitte ta hannun Ammonawa, ka ɗauki matarsa ta zama matarka.


Zan ba da labarin adalcinka, Zan yi magana a kan cetonka duk yini, Ko da yake ya fi ƙarfin in san shi duka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ