Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 51:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, Sabili da madawwamiyar ƙaunarka. Ka shafe zunubaina, Saboda jinƙanka mai girma!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 51:1
31 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Saboda haka sai ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, Ubangiji kuma kansa ya riƙa wartsakar da ku,


Na shafe zunubanka kamar baƙin girgije, Da girgije kuma zan rufe laifofinka Ka komo wurina, ni ne na fanshe ka.”


Duk da haka, ni ne Allah wanda ya shafe zunubanku, Na kuwa yi haka saboda yadda nake. Ba zan ƙara tunawa da zunubanku kuma ba.


Ka kawar da fuskarka daga zunubaina, Ka shafe duk muguntata.


ya kuma yanke igiyar nan ta Shari'a da ta ɗaure mu da dokokinta, ya ɗauke ta, ya kafe ta da ƙusa a jikin gicciyensa.


Sabili da madawwamiyar ƙaunarka, ka amsa mini, ya Ubangiji, Ka juyo wurina, saboda juyayinka mai girma!


Wata rana da yamma Dawuda ya tashi daga shaƙatawa, yana yawo a kan rufin soron fādarsa, can ya hangi wata kyakkyawar mata tana wanka.


Saboda su ne ya tuna da alkawarinsa, Ya sāke ra'ayinsa saboda ƙaunarsa mai yawa.


Ka amsa mini sa'ad da na yi kira, Ya Allah, madogarata! Lokacin da nake shan wahala, ka zama mai taimakona. Ka yi mini alheri, ka kuma saurari addu'ata!


Ko da ya sa ɓacin rai, Zai ji tausayi kuma, Saboda tabbatacciyar ƙaunarsa mai yawa.


Ka bi da ni bisa ga tabbatacciyar ƙaunarka, Ka koya mini umarnanka.


Amma ya Ubangiji, Allahna, ka taimake ni, Yadda ka alkawarta, Ka cece ni sabili da alherin ƙaunarka.


Ya Ubangiji, na sani ba za ka fasa yi mini jinƙai ba! Ƙaunarka da amincinka za su kiyaye lafiyata kullum.


Amma ni, ina iya zuwa wurinka, Saboda ƙaunarka mai girma, In yi sujada a tsattsarkan Haikalinka, In kuma rusuna maka da bangirma.


Kakanninmu a Masar Ba su fahimci ayyukan Allah masu banmamaki ba, Sau da yawa sukan manta da irin ƙaunar da ya nuna musu, Suka tayar wa Mai Iko Dukka a Bahar Maliya.


Amma ni, zan yi addu'a gare ka, ya Ubangiji, Ka amsa mini, ya Allah, a lokacin da ka zaɓa, Sabili da muhimmiyar ƙaunarka, Saboda kana cika alkawarinka na yin ceto.


Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne mai gafara, amma mu, mun tayar masa.


Ya Ubangiji, ka dube mu daga Sama, wurin da kake cike da tsarki da ɗaukaka. Ina kulawan nan da kake yi mana? Ina ikon nan naka? Ina ƙaunan nan taka da juyayin nan naka? Kada ka watsar da mu.


Zan faɗi ƙaunar Ubangiji marar ƙarewa, Zan yabe shi saboda dukan abin da ya yi mana. Ya sa wa jama'ar Isra'ila albarka mai yawa, Saboda jinƙansa da ƙaunarsa marar matuƙa.


Shi mai alheri ne ga kowa, Yana juyayin dukan abin da ya halitta.


Allah ya manta da yin jinƙai ne? Fushinsa ya maye matsayin juyayinsa ne?


Ya Allahna, ka karkato kunnenka ka ji, ka buɗe idanunka ka ga yadda mu da birnin da ake kira da sunanka muka lalace. Ba cewa muna da wani adalci na kanmu shi ya sa muka kawo roƙe-roƙenmu ba, amma saboda yawan jinƙanka.


Kada ka shafe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.”


Amma ya Ubangiji, Ka san dukan maƙarƙashiyarsu, su kashe ni, Kada ka gafarta musu muguntarsu, kada kuma ka shafe zunubinsu daga gabanka. Ka sa a jefar da su daga gabanka, Ka yi da su sa'ad da kake fushi!”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ