Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 48:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ubangiji mai girma ne, Dole kuwa a yabe shi da girmamawa a birnin Allahnmu, A kan tsattsarkan dutsensa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 48:1
31 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zai zama nan gaba, dutse inda Haikalin Ubangiji yake Zai zama shi ne mafi tsawo duka a cikin duwatsu, Zai fi tuddai tsayi, Mutane kuwa za su riƙa ɗunguma zuwa wurinsa.


Zan koma wurin Sihiyona, in zauna a tsakiyar Urushalima. Za a ce da Urushalima birnin gaskiya, da kuma dutsen Ubangiji Mai Runduna, tsattsarkan dutse.


Ubangiji da girma yake, tilas a ɗaukaka shi, Tilas a fi jin tsoronsa fiye da dukan alloli.


Akwai kogin da yake kawo farin ciki a birnin Allah, Da cikin tsattsarkan Haikali na Maɗaukaki.


Ubangiji mai girma ne, dole ne a fifita yabonsa, Girmansa ya fi ƙarfin ganewa.


Sai na ga tsattsarkan birni kuma, Sabuwar Urushalima, tana saukowa daga Sama daga wurin Allah, shiryayyiya kamar amaryar da ta yi ado saboda mijinta.


Ya birnin Allah, ka kasa kunne, Ga abubuwan banmamaki da ya faɗa a kanka.


Sai aka ji wata murya daga kursiyin, tana cewa, “Ku yabi Allahnmu, ya ku bayinsa, Ku da kuke jin tsoronsa, yaro da babba.”


“Don haka sa'ad da kuka ga mummunan aikin saɓo mai banƙyama, wanda Annabi Daniyel ya faɗa, an tsai da shi a Wuri Mai Tsarki (mai karatu fa yă fahimta),


Ku yabi Ubangiji Allahnmu, Ku yi sujada a bisa dutsensa mai tsarki! Ubangiji Allahnmu Mai Tsarki ne!


Allah ya gina birninsa a bisa tsarkakan tuddai,


Gama kai kaɗai ne Maɗaukaki, ya Allah, Kai kaɗai ne ka aikata abubuwa na banmamaki.


A maimakonsu sai ya zaɓi kabilar Yahuza. Ya zaɓi Dutsen Sihiyona, wanda yake ƙauna ƙwarai.


Ya Allah, dole mutane su yabe ka a Sihiyona, Tilas su ba ka abin da suka alkawarta.


Allah yana zaune kan kursiyinsa mai tsarki, Yana mulkin al'ummai,


Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, Kullum a shirye yake yă yi taimako a lokacin wahala.


Ya ce, “A bisa Sihiyona, dutsena tsattsarka, Na naɗa sarkina.”


Amma ku kun iso Ɗutsen Sihiyona ne, da birnin Allah Rayayye, Urushalima ta Sama, wurin dubban mala'iku.


“Amma za a sami waɗanda za su tsira daga Dutsen Sihiyona, Dutsen zai zama wuri ne mai tsarki. Jama'ar Yakubu za ta mallaki mallakarta.


Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, “Nan gaba za su sāke yin magana a ƙasar Yahuza da biranenta a sa'ad da na mayar musu da dukiyarsu. “ ‘Ubangiji ya sa maka albarka, Ya wurin zaman adalci, Ya tsattsarkan tudu!’


A wannan rana za a busa ƙaho don a kirawo Isra'ilawan da suke zaman baƙunci a Assuriya da Masar. Za su zo su yi wa Ubangiji sujada a Urushalima a tsattsarkan dutsensa.


Ubangijinmu mai girma ne, Mai Iko Dukka, Saninsa ya fi gaban aunawa.


Ina yabonka, ya Ubangiji saboda ka cece ni, Ka kuwa hana magabtana su haɗiye ni.


Waɗannan Lawiyawa kuma, wato Yeshuwa, da Kadmiyel, da Bani, da Hashabnaiya, da Sherebiya, da Hodiya, da Shebaniya, da Fetahiya su ne suka yi kiran sujada, suka ce, “Ku miƙe tsaye, ku yabi Ubangiji Allahnku, Ku yabe shi har abada abadin. Bari kowa ya yabi maɗaukakin sunanka, ya Ubangijii, Ko da yake ba yabon da ɗan adam zai yi har ya isa.”


Kamar yadda kishimi yake marmarin ruwan sanyi daga rafi, Haka nake marmarinka, ya Allah.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ