Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 42:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Ina jin ƙishinka, ya Allah, ya Allah Mai Rai, Yaushe zan tafi in yi sujada a gabanka?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 42:2
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya Allah, kai ne Allahna, Ina sa zuciya gare ka. Duk niyyata ta nemanka ce, Raina yana ƙishinka, Kamar bussasshiyar ƙasa, Wadda ta zozaye, ba ta da ruwa.


Kwana guda da za a yi a Haikalinka, Ya fi kwana dubu da za a yi a wani wuri dabam. Na gwammace in tsaya a ƙofar Haikalin Allahna, Da in zauna a gidajen mugaye.


Abu guda nake roƙo a wurin Ubangiji, Abu ɗaya kaɗai nake bukata, Shi ne in zauna a masujadar Ubangiji, In yi ta al'ajabin alherinsa Dukan kwanakin raina, In roƙi biyarwarsa a can.


Sa'an nan, sai ya nuna mini kogin ruwan rai, yana ƙyalli kamar ƙarau, yana gudana daga kursiyin Allah, shi da Ɗan Rago,


A ranar ƙarshe ta idin, wato babbar ranar, sai Yesu ya tsaya, ya ɗaga murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa yă zo gare ni yă sha.


A can nake so in kasance! Ina marmarin farfajiyar Haikalin Ubangiji. Da farin ciki mai yawa zan raira waƙa ga Allah Mai Rai.


Masu murna ne waɗanda suke zaune a Haikalinka, Kullum suna raira yabonka!


Sa'an nan zan tafi wurin bagadenka, ya Allah, Zuwa gare ka, kai wanda kake sa ni in yi murna da farin ciki, In raira waƙar yabo a gare ka da garayata, Ya Allah, Allahna!


Da ma na san inda zan same shi, In kuma san yadda zan kai wurinsa,


Mutanena sun yi zunubi iri biyu, Sun rabu da ni, ni da nake maɓuɓɓugar ruwan rai, Sun haƙa wa kansu tafkunan ruwa, hudaddu, Waɗanda ba za su iya ajiye ruwa ba.


Domin su da kansu suke ba da labarin irin ziyartarku da muka yi, da kuma yadda kuka rabu da gumaka, kuka juyo ga Allah, domin ku bauta wa Allah Rayayye na gaskiya,


Yadda Uba kansa yake tushen rai, haka ya sa Ɗan ya zama tushen rai.


Sukan yi ta ƙara jin ƙarfi a cikin tafiyarsu, Za su kuwa ga Allahn alloli a Sihiyona!


Sau uku a shekara mazaje za su gabatar da kansu a gaban Ubangiji.


Ina umartar mutanen da suke cikin mulkina su yi rawar jiki, su ji tsoron Allah na Daniyel, “Gama shi Allah ne mai rai, Madawwami, Sarautarsa ba ta tuɓuwa, Mulkinsa kuma madawwami ne.


Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya, Shi Allah mai rai ne, Shi Sarki ne madawwami. Saboda hasalarsa duniya ta girgiza, Al'ummai ba za su iya jurewa da fushinsa ba.


Joshuwa kuma ya ƙara da cewa, “Ta haka za ku sani Allah mai rai yana tsakiyarku, ba makawa kuwa zai kori Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Hiwiyawa, da Ferizziyawa, da Girgashiyawa, da Amoriyawa, da Yebusiyawa a gabanku.


Madawwamiyar ƙaunarka ta fi rai kansa, Saboda wannan zan yabe ka.


Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka. Kai kaɗai ne bukatarmu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ