Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 32:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Saboda haka dukan jama'arka masu biyayya, Za su yi addu'a gare ka, lokacin bukata. Sa'ad da babbar rigyawa ta malalo, Ba za ta kai wurinsu ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Saboda haka bari duk mai tsoron Allah yă yi addu’a gare ka yayinda kake samuwa; tabbatacce sa’ad da manyan ruwaye suka taso, ba za su kai wurinsa ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 32:6
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ku juyo wurin Ubangiji, ku yi addu'a gare shi, Yanzu da yake kusa.


Sa'ad da kuke bi ta cikin ruwa mai zurfi, Zan kasance tare da ku, Wahala ba za ta fi ƙarfinku ba. Sa'ad da kuke bi ta cikin wuta, ba za ku ƙuna ba, Wuyar da ta same ku ba za ta cuce ku ba.


Domin ya ce, “Na saurare ka a lokacin samun karɓuwa, Na kuma taimake ka a ranar ceto.” Ga shi, yanzu ne lokacin samun karɓuwa! Ga shi kuma, yau ce ranar ceto!


Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba. Inda nake kuwa ba za ku iya zuwa ba.”


Sa'an nan za ku kira gare ni, amma ba za ku same ni ba. Za ku neme ni a ko'ina, amma ba za ku same ni ba.


Ku tuna fa, Ubangiji ne ya zaɓe ni domin in zama nasa, Ya kuma ji ni lokacin da na yi kira gare shi.


Ka sunkuyo daga Sama, Ka tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi, ka cece ni, Ka cece ni daga ikon baƙi,


Zurfafan tekuna suna kiran junansu, Matsirgar ruwa na Allah kuwa suna ta ruri! Igiyoyin ruwa na baƙin ciki Suka yi wa raina ambaliya.


Ya koya mini raira sabuwar waƙa, Waƙar yabon Allahnmu. Da yawa idan suka ga wannan za su tsorata, Za su kuwa dogara ga Ubangiji.


yana koya mana mu ƙi rashin bin Allah da mugayen sha'awace-sha'awacen duniya, mu kuma yi zamanmu a duniyar nan da natsuwa, da adalci, da kuma bin Allah,


shi da yake yi mana ta'aziyya a dukan wahalarmu, domin mu kuma mu iya ta'azantar da masu shan kowace irin wahala, da ta'aziyyar nan da mu ma muka samu a gun Allah.


Ubangiji ya ce wa jama'arsa, “Idan lokacin da zan cece ku ya yi, zan nuna muku alheri. Zan ji kukanku in taimake ku. Zan tsare ku in kiyaye ku, Zan kuwa yi wa dukan mutane alkawari ta wurinku. Zan bar ku ku sāke zama a ƙasarku wadda take kufai a yanzu.


Duk da haka an yi mini jinƙai musamman, don ta kaina, ni babbansu, Yesu Almasihu yă nuna cikakken haƙurinsa, in zama gurbi ga waɗanda a nan gaba za su gaskata da shi su sami rai madawwami.


Mutum dubu za su fāɗi daura da kai, Dubu goma kuma za su fāɗi dama da kai, Amma kai, ba za a cuce ka ba.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ