Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 32:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Mai farin ciki ne mutumin da aka gafarta masa zunubansa, Mai farin ciki ne kuma wanda aka gafarta masa laifofinsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Mai farin ciki ne shi wanda aka gafarta masa laifofinsa, wanda aka shafe zunubansa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 32:1
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Na shafe zunubanka kamar baƙin girgije, Da girgije kuma zan rufe laifofinka Ka komo wurina, ni ne na fanshe ka.”


Ka gafarta wa jama'arka zunubansu, Ka kuwa gafarta musu dukan kuskurensu,


Duk da haka, ni ne Allah wanda ya shafe zunubanku, Na kuwa yi haka saboda yadda nake. Ba zan ƙara tunawa da zunubanku kuma ba.


Albarka tā tabbata ga masu wanke rigunansu, domin su sami izinin ɗiba daga itacen rai, su kuma shiga birnin ta ƙofa.


Ubangiji ya ce, “Yanzu fa, bari mu daidaita al'amarinmu. Duk kun yi ja wur da zunubi, amma zan wanke ku, ku yi fari fat kamar auduga. Zai yiwu zunubinku ya sa ku zama ja wur, amma za ku yi fari fat kamar farin ulu.


Mai farin ciki ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, Wanda bai juya ga gumaka ba, Ko ya haɗa kai da masu sujada ga allolin karya.


Masu farin ciki ne waɗanda suke biyayya da umarnansa, Waɗanda kullayaumi suke aikata abin da yake daidai!


Amma ya ce, “I, amma albarka tā fi tabbata ga waɗanda suke jin Maganar Allah, suke kuma kiyaye ta.”


Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah.” Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al'amura, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai.


Kamar yadda kishimi yake marmarin ruwan sanyi daga rafi, Haka nake marmarinka, ya Allah.


Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai mai albarka ne, Saminu, ɗan Yunusa! Domin ba ɗan adam ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin Sama.


Mai farin ciki ne wanda yake tsoron Ubangiji, Wanda yake zamansa bisa ga umarnansa!


Masu farin ciki ne jama'ar da suke yi maka sujada, suna raira waƙoƙi, Waɗanda suke zaune a hasken alherinka.


Masu farin ciki ne waɗanda suka dogara gare ka, Ya Allah Mai Runduna!


Me ya sa kake fariya da muguntarka, Ya kai, babban mutum? Ƙaunar Allah tana nan a koyaushe.


Kwanyata ta cika da kyawawan kalmomi, Lokacin da nake tsara waƙar sarki, Harshena kuwa kamar alkalami ne na ƙwararren marubuci.


Ka ji addu'ata, ya Allah, Kada ka ƙi jin roƙona!


Kada ka shafe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.”


Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce masa, “Ubangiji ya gafarta maka, ba za ka mutu ba.


Ya gafarta dukan zunubaina, Ya kuma warkar da dukan cuce-cucena.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ