Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 3:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Na yi kira wurin Ubangiji domin taimako, Ya kuwa amsa mini daga tsattsarkan dutsensa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. Sela

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 3:4
29 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Na yi addu'a ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini, Ya kuɓutar da ni daga dukan tsorona.


Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu, Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala, Zan cece su in girmama su.


Zan amsa addu'o'insu tun ma kafin su gama yin addu'a gare ni.


Marasa galihu suka yi kira gare shi, ya kuwa amsa. Ya cece su daga dukan wahalarsu.


In waninku yana shan wuya, to, sai ya yi addu'a, in kuma waninku yana murna, to, sai ya yi waƙar yabon Allah.


“Ku yi ta roƙo, za a ba ku. Ku yi ta nema, za ku samu. Ku yi ta ƙwanƙwasawa, za a kuwa buɗe muku.


Ka aiko da haskenka, da gaskiyarka, Bari su bishe ni, Su kawo ni Sihiyona, tsattsarkan tudunka, Su kawo ni Haikalinka, inda zatinka yake!


Ya ce, “A bisa Sihiyona, dutsena tsattsarka, Na naɗa sarkina.”


Ka amsa mini sa'ad da na yi kira gare ka, Da ƙarfinka ka ƙarfafa ni.


Ku yabi Ubangiji Allahnmu, Ku yi sujada a bisa dutsensa mai tsarki! Ubangiji Allahnmu Mai Tsarki ne!


Ku yi kira gare ni sa'ad da wahala ta zo, Zan cece ku, Ku kuwa za ku yabe ni.”


Bayan waɗannan al'amura, maganar Ubangiji ta zo ga Abram cikin wahayi cewa, “Abram, kada ka ji tsoro, ni ne garkuwarka, kana da lada mai yawa.”


Na yi kira ga Ubangiji, Yakan cece ni daga magabtana, Yabo ya tabbata ga Ubangiji!


Ta haka zan ci nasara a kan magabtana da suke kewaye da ni. Da sowar farin ciki mai yawa zan miƙa sadakoki a Haikalinsa! Zan raira waƙa, in yabi Ubangiji!


Ubangiji yakan kiyaye ni, yă tsare ni. Na dogara gare shi. Ya taimake ni, don haka ina murna, Ina raira masa waƙoƙin yabo.


Ya jama'ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci! Ku faɗa masa dukan wahalarku, Gama shi ne mafakarmu.


Masu farin ciki ne waɗanda suka dogara gare ka, Ya Allah Mai Runduna!


Ka faɗa wa amintattun bayinka a wahayin da ka nuna musu tun da daɗewa, ka ce, “Na sa kambin sarauta a kan shahararren soja, Na ba da gadon sarauta ga wanda aka zaɓa daga cikin jama'a.


Kai ne kake kāre ni, kake kuma kiyaye ni, Ina sa zuciya ga alkawarinka.


Shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci.


Ka kuwa ji muryata. Kada ka rufe kunnenka ga jin kukana na neman taimako.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ