Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 2:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Sarakunan duniya sun yi tayarwa, Masu mulkinsu suna shirya maƙarƙashiya tare, Gāba da Ubangiji da zaɓaɓɓen sarkinsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 2:2
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

To, sai manyan firistoci da 'yan majalisa duka suka nemi shaidar zur da za a yi wa Yesu don su sami dama su kashe shi.


Da gari ya waye sai duk manyan firistoci da shugabannin jama'a suka yi shawara a kan Yesu su kashe shi.


Kana ƙaunar abin da yake daidai, Kana ƙin abin da yake mugu. Saboda haka Allah, Allahnka, ya zaɓe ka, Ya kuwa kwararo maka farin ciki mai yawa fiye da kowa.


wato labarin Yesu Banazare, yadda Allah ya shafe shi da Ruhu Mai Tsarki da kuma iko, da yadda ya riƙa zagawa na aikin alheri, yana warkar da duk waɗanda Iblis ya matsa wa, domin Allah yana tare da shi.


Hikima, da haziƙanci, da basira, ba kome suke ba gāba da Ubangiji.


Sai ya fara samo ɗan'uwansa Bitrus, ya ce masa, “Mun sami Almasihu,” wato shafaffe.


Kada ka manta da hargowar maƙiyanka, Kada ka manta da hayaniyar da magabtanka suke ta yi.


Sarakuna suka tattaru, Suka zo Dutsen Sihiyona,


Yanzu ku kasa kunne gare ni, ku sarakuna, Ku mai da hankali, ku mahukunta!


Domin wanda Allah ya aiko, zantuttukan Allah yake faɗa, gama Allah yana ba da Ruhu ba da iyakancewa ba.


Na zaɓi bawana Dawuda, Na naɗa shi sarkinku.


Amma ka tuna fa, ya Ubangiji, abokan gābanka suna yi maka ba'a, Su wawaye ne waɗanda suke raina ka.


Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, gama ya ji gunagunin da kuka yi a kansa, gama wane, mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”


Kā ƙaunaci aikin adalci, kā ƙi aikin sāɓo. Saboda haka Allah, wato, Allahnka, ya shafe ka Da man farin ciki fiye da tsararrakinka.”


Nan take waɗansu Farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ai, sai ka tashi, ka fita daga nan, gama Hirudus yana son kashe ka.”


Da Hirudus ya ga masanan nan sun mai da shi wawa, sai ya hasala ƙwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan nan.


Ubangiji ya saukar mini da ikonsa. Ya zaɓe ni, ya aike ni Domin in kawo albishir mai daɗi ga talakawa, In warkar da waɗanda suka karai a zuci, In yi shelar kwance ɗaurarru, Da kuma 'yanci ga waɗanda suke cikin kurkuku.


Ubangiji yana damanka, Zai kori sarakuna a ranar da ya husata.


Sai ya fāɗi, ya kuma ji wata murya tana ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”


Sai manyan firistoci da shugabannin jama'a suka taru a gidan babban firist, mai suna Kayafa.


Da suka gan shi sai suka yi mamaki, Suka tsorata suka gudu.


Su ne mutanen Edom, da Isma'ilawa, Da mutanen Mowab, da Hagarawa,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ