Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 18:7 - Littafi Mai Tsarki

7 Sai duniya ta raurawa ta girgiza, Harsashin duwatsu suka jijjigu, suka girgiza Saboda Allah ya husata!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 18:7
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Bayan sun yi addu'a, wurin da suke a tattare ya raurawa. Sai duk aka cika su da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta faɗar maganar Allah gabagaɗi.


Sai kuwa aka yi wata babbar rawar ƙasa, domin wani mala'ikan Ubangiji ne ya sauko daga Sama, ya zo ya mirgine dutsen, ya zauna a kai.


Da na duba duwatsu, sai na ga suna makyarkyata, Dukan tuddai kuma suna rawar jiki, su yi gaba su yi baya.


Ya Ubangiji, sa'ad da ka bar duwatsun Seyir, Sa'ad da ka fito daga jihar Edom, Ƙasa ta girgiza, Ruwan sama ya zubo daga sararin sama, I, gizagizai suka kwararo da ruwa.


Gama fushina ya kama wuta, Tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za ta cinye duniya da dukan amfaninta, Za ta kama tussan duwatsu.


Ko da zan yi annabci, ina kuma fahimtar dukkan asiri, da dukkan ilimi, ko da kuma ina da matuƙar bangaskiya, har yadda zan iya kawar da duwatsu, muddin ba ni da ƙauna, to, ni ba kome ba ne.


A wannan rana ƙafafunsa za su tsaya a bisa Dutsen Zaitun wanda yake wajen gabas da Urushalima. Dutsen Zaitun zai tsage biyu daga gabas zuwa yamma, ya zama babban kwari. Sashi guda na dutsen zai janye zuwa wajen kudu. Ɗaya sashin kuma zai janye zuwa wajen arewa.


Duwatsu sun gan ka, sun ƙame, Ruwaye masu hauka suka gudu. Zurfi kuma ya ta da muryarsa, Raƙuman ruwansa sun tashi.


Ya tsaya, ya auna duniya, Ya duba, sai ya girgiza al'umman duniya. Sa'an nan madawwaman duwatsu suka farfashe, Madawwaman tuddai kuma suka zama bai ɗaya. Haka hanyoyinsa suke tun adun adun.


Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, Ko da duniya za ta girgiza, Duwatsu kuma su fāɗa cikin zurfafan teku,


Amma yana ƙin masu aikata mugunta, Saboda haka har mutanensu sukan manta da su.


Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai, Yakan ceci waɗanda suka fid da zuciya.


Ka ƙyale ni ko zan sami kwanciyar rai, Kafin in tafi, ai, tawa ta ƙāre.”


Ya fisshe ni daga rami mai hatsari! Ya aza ni a kan dutse lafiya lau. Ya kawar mini da tsoro.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ