Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 18:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Na yi kira ga Ubangiji, Yakan cece ni daga magabtana, Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 18:3
26 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu, Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala, Zan cece su in girmama su.


Yă cece mu daga abokan gābanmu, Har ma daga dukan maƙiyanmu.


Ubangiji mai girma ne, dole ne a fifita yabonsa, Girmansa ya fi ƙarfin ganewa.


Ya jama'ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci! Ku faɗa masa dukan wahalarku, Gama shi ne mafakarmu.


Na yi kira ga Ubangiji, Ya cece ni daga abokan gābana. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!


Ubangiji da girma yake, tilas a ɗaukaka shi, Tilas a fi jin tsoronsa fiye da dukan alloli.


Amma ina kira ga Allah, yă taimake ni, Ubangiji kuwa zai cece ni.


Ku yi kira gare ni sa'ad da wahala ta zo, Zan cece ku, Ku kuwa za ku yabe ni.”


Waɗannan Lawiyawa kuma, wato Yeshuwa, da Kadmiyel, da Bani, da Hashabnaiya, da Sherebiya, da Hodiya, da Shebaniya, da Fetahiya su ne suka yi kiran sujada, suka ce, “Ku miƙe tsaye, ku yabi Ubangiji Allahnku, Ku yabe shi har abada abadin. Bari kowa ya yabi maɗaukakin sunanka, ya Ubangijii, Ko da yake ba yabon da ɗan adam zai yi har ya isa.”


“Macancanci ne kai, ya Ubangiji Allahnmu, Kă sami ɗaukaka, da girma, da iko, Domin kai ne ka halicci dukkan abubuwa, Da nufinka ne suka kasance aka kuma halicce su.”


A sa'an nan ne zai zamanto kowa ya yi addu'a da sunan Ubangiji zai sami ceto.’


Ina misalin darajarka, ya Allah! Ina misalin ɗaukakarka a sa'ad da ka komo daga kan duwatsu, Daga korar abokan gābanka!


Ubangiji mai girma ne, Dole kuwa a yabe shi da girmamawa a birnin Allahnmu, A kan tsattsarkan dutsensa.


Na yi kira wurin Ubangiji domin taimako, Ya kuwa amsa mini daga tsattsarkan dutsensa.


Ka kiyaye ni daga tarkon da aka kafa domina, Kai ne inuwata.


Har yaushe dukanku za ku fāɗa wa wani don ku yi nasara da shi, Kamar rusasshen garu, Ko kuma dangar da ta fāɗi?


Ka zama mini lafiyayyiyar mafaka, Da kagara mai ƙarfi, domin ka tsare ni, Kai ne mafakata da kāriyata.


Ya iya ce wa Ubangiji, “Kai ne kāriyata, da mai kiyaye ni! Kai ne Allahna, a gare ka nake dogara!”


Yabo ya tabbata ga Ubangiji, mai kiyaye ni, Ya hore ni don yaƙi, Ya kuwa shirya ni don yaƙi.


“Ya Ubangiji, ƙarfina da kagarata, Mafakata a ranar wahala, A gare ka al'ummai za su zo, Daga ƙurewar duniya, su ce, ‘Kakanninmu ba su gāji kome ba, sai ƙarya, Da abubuwan banza marasa amfani.’


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ