Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 143:8 - Littafi Mai Tsarki

8 A gare ka nake dogara, Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka. Addu'ata ta hau zuwa gare ka, Ka nuna mini hanyar da zan bi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Bari safiya ta kawo mini maganar ƙaunarka marar ƙarewa, gama na sa zuciyata a gare ka. Ka nuna mini hanyar da zan bi, gama a gare ka na miƙa raina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 143:8
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Ubangiji, wanda ya fanshe ku, ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, Wanda yake so ya koya muku domin amfanin kanku, Ya kuwa nuna muku hanyar da za ku bi.


Allah yana zaune cikin birnin, Ba kuwa za a hallaka birnin ba, faufau. Da asuba Allah zai kawo musu gudunmawa.


Ubangiji ya ce, “Zan koya maka hanyar da za ka bi, Zan koya maka, in kuma ba ka shawara.


Idan kuka kauce daga hanya zuwa dama ko hagu, za ku ji muryarsa a bayanku yana cewa, “Ga hanyan nan, ku bi ta.”


Amma zan raira waƙa a kan ikonka, Kowace safiya zan raira waƙa da ƙarfi Ga zancen madawwamiyar ƙaunarka. Kai mafaka ne a gare ni, Wurin ɓuya a kwanakin wahala.


Kai ne Allahna, Ka koya mini in aikata nufinka. Ka sa in sami alherin Ruhunka. Ka bi da ni a hanyar lafiya.


Ka koya mini abin da ya kamata in yi, ya Ubangiji, Ka bi da ni kan lafiyyiyar hanya, Domin ina da magabta da yawa.


Ka cika mu da madawwamiyar ƙaunarka a kowace safiya, Don mu raira waƙoƙin murna dukan kwanakin ranmu.


Bari mu roƙi Allah na Sama, Muna miƙa hannuwanmu sama, mu ce,


Ka sa bawanka yă yi murna, ya Ubangiji, Saboda addu'o'ina sun hau zuwa gare ka.


Fushinsa ba ya daɗewa, Alherinsa kuwa har matuƙa ne. Mai yiwuwa ne yă zama ana kuka da dare, Amma a yi murna da safe.


Ka fassara mini dokarka, ni kuwa zan yi biyayya da ita, Zan kiyaye ta da zuciya ɗaya.


Kai ne ka halicce ni, ka kuma kiyaye ni lafiya, Ka ba ni ganewa, don in koyi dokokinka.


Ubangiji ya nuna madawwamiyar ƙaunarsa kowace rana! Ni ma in raira yabo gare shi kowane dare, In yi addu'a ga Allah, wanda ya ba ni rai.


Ina da abokan gāba da yawa, ya Ubangiji, Ka bi da ni in aikata nufinka, Ka kuma fayyace mini hanyarka domin in bi ta!


Mu nace domin mu san Ubangiji Zuwansa tabbatacce ne kamar wayewar gari. Zai zo wurinmu kamar ruwan sama, Kamar ruwan bazara da yake shayar da ƙasa.”


Manowa kuma ya ce, “Lokacin da maganarka ta cika, wane irin yaro ne zai zama, me kuma za mu yi?”


Dawuda kuma ya ce, “Mutanen Kaila za su bashe ni da mutanena a hannun Saul?” Ubangiji ya ce masa, “Za su bashe ku.”


Ka yi mini kāriya, ka cece ni, Gama na zo wurinka neman kāriya.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ