Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 141:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Ka tsare ni daga son yin mugunta, Ko kuma in haɗa kai da mugaye cikin muguntarsu, Ka sa kada in taɓa yin tarayya da su a bukukuwansu!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Kada ka bar zuciyata ta juya ga yin abin da yake mugu, ta sa kai ga aikata mugayen ayyuka tare da mutane masu aikata mugunta; kada ka bari in ci abincinsu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 141:4
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kada ka kai mu wurin jaraba, Amma ka cece mu daga Mugun.’


Ka sa ni in so yin biyayya da ka'idodinka, Fiye da samun dukiya.


Don me ka bari muka ɓata daga al'amuranka? Don me ka bari muka taurare, har muka bar binka? Ka komo, domin darajar waɗanda suke bauta maka, domin kuma mutanen da suke naka ne a koyaushe.


Saboda haka, sai ku fito daga cikinsu, Ku keɓe, in ji Ubangiji, Kada ku ko taɓa wani abu marar tsarki, Ni kuwa in yi na'am da ku,


Kada fa a yaudare ku! “Zama da mugaye yakan ɓata halayen kirki.”


Ka sa zukatanmu su juyo gare ka, mu yi tafiya cikin tafarkunka, mu kiyaye umarnanka, da ka'idodinka da dokokinka, waɗanda ka umarci kakanninmu.


Duk wanda ake jarabta, kada ya ce Allah ne yake jarabtarsa, gama ba shi yiwuwa a jarabci Allah da mugunta, shi kansa kuwa ba ya jarabtar kowa.


To, duk abin da kuke yi, ko ci, ko sha, ku yi kome saboda ɗaukakar Allah.


Sai na ji wata murya daga Sama, tana cewa, “Ku fito daga cikinta, ya ku jama'ata, Kada zunubanta su shafe ku, Kada bala'inta ya taɓa ku.


Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku zuciyar ganewa, ko idanun gani, ko kunnuwan ji ba.


Ubangiji ya ce masa, ‘Ta wace hanya?’ Sai ruhun ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakin dukan annabawansa.’ Sai Ubangiji ya ce, ‘Ba shakka za ka yaudare shi, za ka yi nasara, sai ka tafi.’ ”


“Amma Sihon, Sarkin Heshbon, ya ƙi yarda mu wuce, gama Ubangiji Allahnku ya riga ya taurare hankalinsa da zuciyarsa don ya bashe shi a hannunku, kamar yadda yake a yau.


Waɗannan mata sukan gayyaci mutanen zuwa wajen shagalin tsafinsu. Isra'ilawa kuwa sukan ci abinci, su kuma yi sujada ga gumaka.


Ya tafi ya kamo su, ya kawo su ga mahaifiyarsa, mahaifiyarsa kuwa ta shirya abinci mai daɗi irin wanda mahaifinsa yake so.


Annabin kuwa ya ce wa sarki, “Ko da za ka ba ni rabin gidanka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuma zan ci abinci ko in sha ruwa a wurin nan ba.


Kada ka kāshe ni tare da mugaye, Tare da masu aikata mugunta, Mutane waɗanda maganarsu kamar ta zumunci ce, Amma zukatansu cike suke da ƙiyayya.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ