Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 140:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne Allahna. Ka ji kukana na neman taimako, ya Ubangiji!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 140:6
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Amma a gare ka na dogara, ya Ubangiji, Kai ne Allahna.


Na ce wa Ubangiji, “Kai ne Ubangijina, Dukan kyawawan abubuwan da nake da su Daga gare ka suke.”


Ya Ubangiji, na kawo kuka gare ka na neman taimako, Ya Ubangiji, kai ne mai kiyaye ni, Kai kaɗai nake so a rayuwata duka.


Kai kaɗai nake so, ya Ubangiji, Na yi alkawari in yi biyayya da dokokinka.


Sulusi ɗayan da ya ragu kuwa zan tura cikin wuta, Zan tace su da wuta kamar yadda akan tace azurfa, Zan gwada su kamar yadda akan gwada zinariya. Za su kira gare ni, Zan kuwa amsa musu, Zan ce, ‘Su jama'ata ne,’ Su kuma za su ce, ‘Ubangiji shi ne Allahnmu.’ ”


Na ce, “Ubangiji shi ne nawa, Saboda haka zan sa zuciya gare shi.”


Ya Ubangiji ka ji addu'ata, Ka kasa kunne ga roƙona! Kai adali ne mai aminci, Don haka ka amsa mini!


Ka ji kukana, ya Ubangiji, Ka kasa kunne ga kiran da nake yi na neman taimako!


Ina ƙaunar Ubangiji, saboda yana jina, Yana kasa kunne ga addu'o'ina.


Ya iya ce wa Ubangiji, “Kai ne kāriyata, da mai kiyaye ni! Kai ne Allahna, a gare ka nake dogara!”


Ina shan wahala, ya Allah, ka ji addu'ata! Ina jin tsoro, ka cece ni daga maƙiyana!


A shirye nake, ya Allah, Na shirya sosai! Zan raira waƙoƙi in yabe ka!


Na duba kewaye da ni, sai na ga ba ni da wanda zai taimake ni, Ba wanda zai kiyaye ni, Ba kuwa wanda ya kula da ni.


Bari a ji kururuwa daga gidajensu, Saboda maharan da ka aika musu farat ɗaya, Gama sun haƙa rami don in fāɗa, Sun kafa wa ƙafafuna tarkuna.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ