Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 11:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Yakan aukar da garwashin wuta Da kibritu mai cin wuta a kan mugaye, Yakan hukunta su da harshen wuta mai ƙuna.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 11:6
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zan hukunta shi da annoba da kuma zub da jini. Zan yi masa ruwa da ƙanƙara, da wuta, da kibritu za a makaka a kansa da rundunarsa, da dukan jama'ar da suke tare da shi.


Sai Ubangiji ya yi ta zuba wa Saduma da Gwamrata wutar kibritu daga sama,


“Saboda haka ni Ubangiji Allah na ce da hasalata zan sa babban hadiri mai iska, da rigyawa, da manyan ƙanƙara su hallaka shi.


amma a ranar da Lutu ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da duwatsun wuta daga sama, aka hallaka su duka.


Ubangiji yana riƙe da ƙoƙo, Cike da sabon ruwan inabi mai ƙarfi, Yana zuba shi, dukan mugaye kuwa suna ta sha, Suka shanye shi ƙaƙaf.


Bari ya ci duk irin abin da yake so! Allah zai hukunta shi da hasala da fushi.


Yanzu kowa zai iya zama a alfarwarsa, Bayan da an karkashe ƙwayoyin cuta da farar wuta.


Sai Yesu ya ce wa Bitrus, “Mai da takobinka kube. Ba sai in sha ƙoƙon da Uba ya ba ni in sha ba?”


A maimakon daraja, za ka sha ƙasƙanci. Ka sha kai da kanka, ka yi tangaɗi. Ƙoƙon da yake a hannun Ubangiji zai faɗo a kanka, Kunya za ta rufe darajarka.


Ya aiki ƙanƙara da tsawa a bisa ƙasarsu Maimakon ruwan sama.


Ya Urushalima, ki farka! Ki tashi da kanki, ki miƙe! Kika sha ƙoƙon hukunci wanda Ubangiji, cikin fushinsa, ya ba ki ki sha, Kika shanye shi, ya kuwa sa ki yi tangaɗi!


Kai ne kaɗai, nake da shi, ya Ubangiji, Kai ne kake biyan dukan bukatata, Raina yana hannunka.


Ubangiji Allahnku ya kāre ku ya ce, “Ina ɗauke ƙoƙon da na ba ku cikin fushina. Ba za ku ƙara shan ruwan inabin da zai sa ku yi tangaɗi ba.


Sama'ila kuwa ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman nan da na ba ka, wanda na ce ka ajiye shi dabam.”


Duk lokacin da Elkana ya miƙa hadayarsa, sai ya ba Feninna da 'ya'yanta mata da maza nasu rabo.


Daga teburin da yake a gabansa aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Biliyaminu ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.


An binne masa tarko a ƙasa, An kafa masa tarko a hanyarsa.


Sa'an nan Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama, Aka ji muryar Maɗaukaki. Ƙanƙara da garwashin wuta suka sauko.


Tilas ne mugu yă sha wahala, Amma masu dogara ga Ubangiji, Madawwamiyar ƙaunarsa tana kiyaye su.


Ubangiji ya ce, “Wannan shi ne rabonku, Rabon da na auna muku, ni Ubangiji na faɗa. Domin kun manta da ni, kun dogara ga ƙarairayi,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ