Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 11:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa, Yana da kursiyinsa a Sama. Yana kallon dukan mutane Yana sane da abin da suke yi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon ’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 11:4
28 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ya kafa kursiyinsa a Sama, Shi yake sarautar duka.


A shan wahalata na kira ga Ubangiji, Na yi kira ga Allahna domin neman taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.


Ubangiji ya yi dariya daga kan kursiyinsa can Sama, Ya mai da su abin dariya.


“Amma Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa, Bari duniya ta yi tsit a gabansa.”


Ubangiji ya ce, “Sama kursiyina ce, duniya kuwa matashin sawuna ce. Daga nan wane irin gida za ku iya ginawa domina, wane irin wuri ne kuma zan zauna?


“Mutum ya iya ɓoye kansa a wani lungu Inda ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji. “Ashe, ban cika sammai da duniya ba?


Daga Sama Ubangiji ya dubo dukan 'yan adam.


Nan da nan kuwa Ruhu ya iza ni, sai ga wani kursiyi a girke a Sama, da wani a zaune a kai.


Ba wata halittar da za ta iya ɓuyar masa, amma kowane abu a fili yake, a shanye sosai a gaban idon wannan da za mu ba da lissafi a gabansa.


Shi ne magabci, mai ɗaukaka kansa, yana gāba da duk abin da ya shafi sunan Allah, ko kuma wanda ake yi wa ibada. Har ma yakan zauna a Haikalin Allah, yana cewa, shi ne Allah.


Duk kuma wanda ya rantse da Haikalin ya rantse da shi, da kuma wanda yake zaune a cikinsa.


Amma ni ina gaya muku, kada ma ku rantse sam, ko da sama, domin ita ce kursiyin Allah,


Har abada yana mulki ta wurin ƙarfinsa, Yana duban al'ummai, Don kada 'yan tawaye su tayar masa!


Idon Ubangiji fa, yana kai da komowa ko'ina a duniya don ya nuna ikonsa ga dukan waɗanda suka dogara gare shi da zuciya ɗaya. Ka yi wauta a cikin wannan al'amari. Tun daga yanzu har zuwa nan gaba za ka yi ta fama da yaƙoƙi.”


Gama tun ranar da na fito da Isra'ilawa ban taɓa zama a cikin ɗaki ba, amma daga alfarwa zuwa alfarwa, daga wannan mazauni kuma zuwa wancan.


“ ‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina, Ƙasa kuwa matashin ƙafata. Wane wuri kuma za ku gina mini? Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna?


Ubangiji yana ganin abin da yake faruwa a ko'ina, yana lura da mu, ko muna aikata alheri ko mugunta.


Bari dukan 'yan adam su yi tsit a gaban Ubangiji, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.


Ni Ubangiji nakan bincike tunani, In gwada zuciya, Domin in sāka wa kowane mutum gwargwadon al'amuransa, Da kuma gwargwadon ayyukansa.


Hakika ka gane, Domin ka san asirin tunanin mutane.


Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona! Ku faɗa wa kowace al'umma abin da ya yi!


Dukanku ku ji, ku al'ummai! Ki kasa kunne, ya duniya, da dukan abin da yake cikinki. Bari Ubangiji Allah Daga Haikalinsa mai tsarki ya zama shaida a kanku.


Ya yiwu Allah ya bar shi ya yi zamansa lafiya, Amma a kowane lokaci zai sa ido a kansa.


Daga Sama Ubangiji ya dubi mutane, Yă ga ko da akwai masu hikima Waɗanda suke yi masa sujada.


Ba wani kamar Ubangiji Allahnmu. Yana zaune a can ƙwanƙolin sama,


Jarraba ni, ya Allah, ka san tunanina, Gwada ni, ka gane damuwata.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ