Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 103:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Ya gafarta dukan zunubaina, Ya kuma warkar da dukan cuce-cucena.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 103:3
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya ce, “In za ku himmantu ku yi biyayya da ni, ni da nake Ubangiji Allahnku, sai ku aikata abin da yake daidai a gare ni, ku kuma kiyaye umarnaina da dokokina duka, to, ba zan sa muku cuce-cuce irin waɗanda na sa wa Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”


Amma aka yi masa rauni saboda zunubanmu, Aka daddoke shi saboda muguntar da muka aikata. Hukuncin da ya sha ya 'yantar da mu, Dūkan da aka yi ta yi masa, ya sa muka warke.


Na roƙi taimako a gare ka, ya Ubangiji Allahna, Ka kuwa warƙar da ni.


Ubangiji, ka warkar da ni, zan kuwa warke, Ka cece ni, zan kuwa cetu, Gama kai ne abin yabona.


Yakan warkar da masu karyayyiyar zuciya, Yakan ɗaure raunukansu.


Addu'ar bangaskiya kuwa, za ta warkar da marar lafiya Ubangiji kuma zai tashe shi, in ma ya yi zunubi, za a gafarta masa.


Duk da haka, ni ne Allah wanda ya shafe zunubanku, Na kuwa yi haka saboda yadda nake. Ba zan ƙara tunawa da zunubanku kuma ba.


Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, an gafarta maka zunubanka.”


Sai Musa ya roƙi Ubangiji, ya ce, “Ina roƙonka, ya Allah, ka warkar da ita.”


Zai fanshi jama'arsa Isra'ila Daga dukan zunubansu.


Ta gare shi ne muka sami fansa albarkacin jininsa, wato yafewar laifofinmu, bisa ga yalwar alherin Allah,


Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce masa, “Ubangiji ya gafarta maka, ba za ka mutu ba.


Ba wanda zai zauna a ƙasarmu har ya ƙara yin kukan yana ciwo, za a kuma gafarta dukan zunubai.


Ni ne mai nuna ƙauna ga dubbai, mai gafarta mugunta, da laifi, da zunubi, wanda ba zai kuɓutar da mai mugunta ba, amma saboda laifin iyaye nakan hukunta 'ya'ya da jikoki har tsara ta uku da ta huɗu.”


Suna cewa, “Yana ciwon ajali, Ba zai taɓa tashi daga gadonsa ba.”


Ya Ubangiji, kai managarci ne, mai yin gafara, Cike kake da madawwamiyar ƙauna ga dukan waɗanda suke yin addu'a gare ka.


Amma kakan gafarta mana, Domin mu zama masu tsoronka.


Ɓacin zuciyata zai juya ya zama salama. Ka ceci raina daga dukan hatsari, Ka gafarta dukan zunubaina.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ