Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Zabura 10:7 - Littafi Mai Tsarki

7 Maganganunsa suna cike da zage-zage, da ƙarairayi, da barazana, Yana da saurin faɗar maganganun ƙiyayya da na mugunta.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Zabura 10:7
29 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ka duba, yadda mugu yake tunanin mugunta a ransa, Yana shisshirya wahala, yana kuma aikata ruɗi.


Ɗanɗana mugunta yana da daɗi a gare shi ƙwarai, Yakan sa wata a bakinsa don ya riƙa jin daɗin tsotsanta.


Ka cece ni daga mugayen abokan gābana, Ka ƙwato ni daga ikon baƙi, Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba, Sukan yi rantsuwar ƙarya.


“Kada ka bar maƙiyana su sami nasara, Ka sa kashedin da suke yi mini yă koma kansu.


Harsunansu kamar macizai masu zafin dafi, Kalmominsu kuwa kamar dafin gamsheƙa ne.


Sukan yi wa waɗansu ba'a, Suna faɗar mugayen abubuwa, Masu girmankai ne su, suna shawara A kan yadda za su zalunci waɗansu.


Sukan wasa harsunansu kamar takuba, Sukan kai bāra da mugayen maganganu kamar kibau.


Zunubi na cikin leɓunansu, maganganunsu na zunubi ne, Da ma a kama su saboda girmankansu, Domin suna la'antarwa, suna ƙarya!


Kana jin daɗin cutar mutane da maganganunka, Ya kai, maƙaryaci!


Maganarsa mugunta ce cike da ƙarairayi, Ba shi da sauran isasshiyar hikima da zai aikata nagarta.


Ku macizai! Yaya za ku iya yin maganar kirki, alhali kuwa ku mugaye ne? Don abin da ya ci rai, shi mutum yake faɗa.


Suna ƙara zalunci a kan zalunci, Yaudara a kan yaudara, Sun ƙi sanina,” in ji Ubangiji.


Ubangiji ya ce, “Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, Ƙarya ce take rinjayar gaskiya a ƙasar. Suna ta cin gaba da aikata mugunta, Ba su kuwa san ni ba.


Ba wanda yake kai ƙara ta gaskiya, ba wanda yake yanke shari'a da adalci. Kuna dogara ga shaidar ƙarya, kuna faɗar ƙarya, kuna ɗaukar ciki na ɓarna, ku haifi mugunta.


Ka kawar da ƙarya nesa da ni. Kada ka ba ni talauci ko dukiya, sai dai ka ba ni abinci daidai da bukatata,


Dukiyar da aka tara ta hanyar rashin gaskiya takan ƙare nan da nan, takan kuma kai ga mutuwa.


Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba, Sukan yi rantsuwar ƙarya.


Ba abin da kuke so, sai ku ƙasƙantar da shi daga maƙaminsa na daraja, Kuna jin daɗin yin ƙarairayi. Kuna sa masa albarka, Amma a zuciyarku la'antarwa kuke yi.


Mugaye, laifi suke yi dukan kwanakinsu, Tun daga ranar da aka haife su suke ta faɗar ƙarya.


Kalmominsa sun fi mai taushi, Amma ƙiyayya tana a zuciyarsa, Kalmominsa sun fi mai sulɓi, Amma suna yanka kamar kakkaifan takobi.


Masu zuwa su gaishe ni ba da zuciya ɗaya suke zuwa ba, Sukan tattara duk mugun labari a kaina Sa'an nan su je su yi ta bazawa ko'ina.


Dukan mutane suna yi wa juna ƙarya, Suna ruɗin junansu da yaudara.


Abin da maƙiyana ke faɗa, Ba abin da za a yarda da shi ba ne, Su dai, so suke su hallakar kawai, Bakinsu kamar buɗaɗɗen kabari yake, Maganganunsu kuwa suna da taushi da kuma yaudara.


Waɗannan su ne irin mutanen da suke shirya tarzoma, su aikata mugunta. Kullum zuciyarsu cike take da ruɗarwa.”


“Kullum a shirye kuke ku hurta mugunta, Ba ku jin nauyin faɗar ƙarya.


Da fushinka ka hallaka su, Ka hallaka su ɗungum. Sa'an nan jama'a za su sani Allah yana mulkin Isra'ila, Mulkinsa ya kai ko'ina a duniya!


Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata, kuna ƙoƙari ku hallakar da matalautan ƙasar.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ