Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Yoshuwa 7:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Ya Ubangiji, me zan ce bayan da Isra'ilawa sun ba da baya ga abokan gābansu?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Yoshuwa 7:8
8 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zan tsaya a wurin tsayawata, In zauna kuma a kan hasumiya, In jira in ji abin da zai ce mini, Da abin da zai amsa a kan kukata.


“Yanzu, me za mu ce bayan wannan, ya Allahnmu, gama mun manta da umarnanka.


Joshuwa ya ce, “Kaitonmu, ya Ubangiji Allah, me ya sa ka haye da jama'an nan zuwa wannan hayin Urdun, don ka bashe mu a hannun Amoriyawa, su hallakar da mu? Da ma mun haƙura, mun yi zamanmu a wancan hayin Urdun.


Gama Kan'aniyawa da dukan mazaunan ƙasar za su ji labari, su kewaye mu, su shafe sunanmu daga duniya, to, me za ka yi don sunanka mai girma?”


Da sojojin da suka ragu suka koma sansani, sai shugabannin Isra'ila suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa Filistiyawa suka ci mu yau? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo ya kasance tare da mu, ya cece mu daga ikon abokan gābanmu.”


Ka sa muka gudu daga gaban abokan gābanmu, Suka ƙwace abin da muke da shi.


Ka sa makamansa su zama marasa amfani, Ka bari a ci shi da yaƙi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ