Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Yoshuwa 24:33 - Littafi Mai Tsarki

33 Ele'azara, ɗan Haruna kuma ya rasu, aka binne shi a Gebeya a garin ɗansa, Finehas, wanda aka ba shi a ƙasar tuddai ta Ifraimu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

33 Eleyazar ɗan Haruna, ya mutu aka binne shi a Gibeya, wurin da aka ba ɗansa Finehas a ƙasar kan tudu ta Efraim.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Yoshuwa 24:33
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Mutanen Isra'ila kuwa suka aiki Finehas, ɗan Ele'azara, firist, wurin Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa a ƙasar Gileyad.


Ele'azara, ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin 'ya'ya mata na Futiyel. Ita kuwa ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan kabilar Lawi bisa ga kabilansu.


Amma shi da yake madawwami ne, yana da matsayinsa na firist wanda ba ya komawa hannun wani.


Dawuda kam, bayan da ya bauta wa mutanen zamaninsa bisa ga nufin Allah, ya yi barci, aka binne shi tare da kakanninsa, ya kuwa ruɓe.


To, ina kakannin nan naku suke? Annabawan fa? Suna da rai har wa yau?


Yakan sa masu hikima su ma su mutu, Haka nan ma wawaye da mutanen banza, Za su mutu su bar dukiyarsu ga zuriyarsu.


Hakika na sani za ka kai ni ga mutuwa, Gidan da aka ƙaddara wa kowane mai rai.


Waɗannan su ne karkasuwar gādon da Isra'ilawa suka karɓa a ƙasar Kan'ana, wanda Ele'azara, firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin iyalan kabilan Isra'ila suka ba su.


Ele'azara, ɗan Haruna, firist, shi zai shugabanci shugabannin Lawiyawa, shi ne kuma zai lura da waɗanda suke aiki a Wuri Mai Tsarki.


Haruna ya auri Elisheba, 'yar Amminadab 'yar'uwar Nashon. Sai ta haifa masa Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar.


Saurayin kuwa ya yi ƙaura daga Baitalami. Sa'ad da yake tafiya sai ya iso gidan Mika, a ƙasar tudu ta Ifraimu.


Akwai wani mutum daga kabilar Ifraimu sunansa Elkana, yana zaune a Rama, a ƙasar tudu ta Ifraimu. Shi ɗan Yeroham ne, jika ga Eliyab, na iyalin Nahat, daga zuriyar Zuf.


Suka bi ta ƙasar tudu ta Ifraimu, suka ratsa ta ƙasar Shalisha, amma ba su same su ba. Suka kuma bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba. Sai suka bi ta ƙasar Biliyaminu, amma ba su same su ba.


Ba haka ba ne, ni dai ina neman mutumin ƙasar tudu ta Ifraimu, wanda ake ce da shi Sheba, ɗan Bikri. Shi ne ya tayar wa sarki Dawuda. Shi kaɗai za ku ba ni, ni kuwa zan janye daga garin.” Macen kuwa ta ce wa Yowab, “To, za a jefar maka kansa ta kan garu.”


Waɗannan su ne hakimai, da kuma lardunan da suke aiki. Ben-hur yana a ƙasar tudu ta Ifraimu. Ben-deker shi ne mai lura da biranen Makaz, da Shalim, da Bet-shemesh, da Elon-bet-hanan. Ben-hesed shi ne mai lura da Arubot, da Soko, da dukan ƙasar Hefer. Ben-abinadab shi ne mai lura da dukan jihar Dor, ya auri Tafat 'yar Sulemanu. Ba'ana ɗan Ahilud shi ne mai lura da biranen Ta'anak da Magiddo, da dukan jihar Bet-sheyan, kusa da garin Zaretan, kudu da garin Yezreyel, har zuwa birnin Abel mehola da birnin Yokmeyam. Ben-geber shi ne mai fura da birnin Ramot-gileyad, da ƙauyukan Yayir da Manassa, waɗanda suke a Gileyad, da kuma yankin Argob, wanda yake a Bashan, duka dai akwai manyan garuruwa sittin masu garu da ƙyamare na tagulla. Abinadab ɗan Iddo shi ne mai lura da birnin Mahanayim. Ahimawaz shi ne mai lura da Naftali, ya auri Basemat 'yar Sulemanu. Ba'ana ɗan Hushai shi ne mai lura da Ashiru da garin Beyalot. Jehoshafat ɗan Faruwa shi ne mai lura da Issaka. Shimai ɗan Ila shi ne mai lura da ƙasar Biliyaminu. Geber ɗan Uri shi ne mai lura da jihar Gileyad wadda Sihon Sarkin Amoriyawa, da Og Sarkin Bashan, suka mallaka. Bayan waɗannan sha biyu akwai hakimi ɗaya da yake kan ƙasar Yahuza.


Gehazi ya ce, “Lafiya ƙalau, maigidana ne ya aiko ni in faɗa maka, yanzu yanzu waɗansu samari biyu daga ƙungiyar annabawa suka zo wurinsa daga ƙasar tudu ta Ifraimu, yana roƙonka, ka ba ni talanti ɗaya na azurfa da rigunan ado guda biyu in kai masa.”


Daga can suka wuce zuwa ƙasar tudu ta Ifraimu, suka zo gidan Mika.


da Abishuwa da Finehas, da Ele'azara, da Haruna babban firist.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ