Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Yoshuwa 23:7 - Littafi Mai Tsarki

7 domin kada ku yi cuɗanya da sauran al'umman da take zaune tare da ku, kada ku ambaci sunayen gumakansu, ko ku rantse da su, ko ku bauta musu, ko ku sunkuya musu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Yoshuwa 23:7
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ku kula da dukan abin da na faɗa muku. Kada a ji bakinku na roƙon kome ga waɗansu alloli.”


“Don me zan gafarce ki? 'Ya'yanki sun rabu da ni, Sun yi rantsuwa da gumaka, Na ciyar da su har sun ƙoshi sosai, Suka yi karuwanci, suka ɗunguma zuwa gidajen karuwai,


Waɗanda suke hanzari zuwa ga gumaka, Za su jawo wa kansu wahala. Ba zan yi tarayya da su da hadayarsu ba. Ba zan yi sujada ga gumakansu ba.


Kada su zauna cikin ƙasarku domin kada su sa ku ku yi mini zunubi, ku bauta wa allolinsu, har abin kuwa ya zamar muku tarko.”


Ku yi nesa da ayyukan duhu na banza da wofi, sai dai ku tona su.


Kada fa a yaudare ku! “Zama da mugaye yakan ɓata halayen kirki.”


Da kuma waɗanda suke durƙusa wa rundunan sama a kan bene, Waɗanda sukan durƙusa, su rantse da Ubangiji, Duk da haka kuma sai su rantse da Milkom,


Kada ka tafi inda mugaye suke tafiya, kada ka bi gurbin mugaye.


Gama idan kun kauce, kun koma da baya, kun haɗa kai da sauran al'umman nan da take tare da ku, har kuka yi aurayya da juna,


Zan kawar da sunayen Ba'al daga bakinta. Ba za a ƙara kiransu da sunayensu ba.


Kada ka rusuna musu, kada kuwa ka bauta musu, gama ni Ubangiji Allahnka, mai kishi ne. Nakan hukunta 'ya'ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina.


Sai ku ji tsoron Ubangiji Allahnku. Shi ne za ku bauta masa, ku rantse da sunansa.


Sai kuma ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa. Ku manne masa, ku yi rantsuwa da sunansa.


Amma ku manne wa Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi har wa yau.


Zai zama kuwa, idan za su himmantu su koyi al'amuran jama'ata, su yi rantsuwa da sunana, su ce, ‘Da zatin Ubangiji,’ kamar yadda suka koya wa jama'ata yin rantsuwa da Ba'al, sa'an nan za a gina su a tsakiyar jama'ata.


Amma idan ba ku kori mazaunan ƙasar daga gabanku ba, to, waɗannan da kuka bari cikinta za su zama haki a idanunku, da ƙayayuwa a kwiyaɓunku. Za su yi ta wahalshe ku da yaƙi.


Kada ku bi waɗansu alloli na al'umman da suke kewaye da ku,


Sai dai Ubangiji ya gafarta mini lokacin da na bi sarki zuwa cikin haikalin Rimmon, gunkin Suriya, don ya yi sujada. Na gaskata Ubangiji zai gafarta mini.”


Suka bauta wa gumaka waɗanda Ubangiji ya ce musu kada su bauta musu.


Amma idan ka juya, ka bar dokokina da umarnaina waɗanda na sa a gabanka, har ka shiga bautar gumaka kana musu sujada,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ