Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




W.Yah 8:11 - Littafi Mai Tsarki

11 Sunan tauraron kuwa Ɗaci. Sulusin ruwa ya zama mai ɗaci, sai mutane da yawa suka mutu saboda shan ruwan, don ɗacinsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 sunan tauraron kuwa Maɗaci. Kashi ɗaya bisa uku na ruwaye ya zama mai ɗaci, mutane da yawa kuma suka mutu saboda shan ruwan, don ɗacinsa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




W.Yah 8:11
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce a kan annabawa, “Ga shi, zan ciyar da su da abinci mai ɗaci, In shayar da su da ruwan dafi. Daga wurin annabawan Urushalima Rashin tsoron Allah ya fito ya mamaye dukan ƙasar.”


Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, zan ciyar da mutanen nan da abinci mai ɗaci, in shayar da su da ruwan dafi.


Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, ta koma ga bauta wa gumakan al'umman nan. Kada a iske wani tushe a cikinku mai ba da 'ya'ya masu dafi, masu ɗaci.


Dawakai sukan yi sukuwa a duwatsu? Ana huɗan teku da garmar shanu? Duk da haka kuka mai da adalci dafi, Kuka mai da nagarta, mugunta.


Abin tausayi ne ku da kuke ɓata shari'a, Kuna hana wa mutane hakkinsu.


Ka tuna da azabata, da galabaitata, Da ɗacin raina, da kumallon da nake fama da shi.


Amma bayan an gama duka, ba abin da za ta bar maka sai baƙin ciki, da azaba.


Mala'ikan farko ya busa ƙahonsa, sai ga ƙanƙara da wuta, gauraye da jini. Aka zuba su a duniya, sai sulusin duniya ya ƙone, sulusin itatuwa suka ƙone, dukkan ɗanyar ciyawa kuma ta ƙone.


Ku kula fa, kada kowa yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai ya tabbata, ya haddasa ɓarna, har ya ɓata mutane masu yawa ta haka,


Ya kewaye ni da yaƙi, Ya rufe ni da baƙin ciki mai tsanani da wahala.


Ita kuwa ta ce musu, “Kada ku kira ni Na'omi, wato mai farin ciki, sai dai Mara, wato mai baƙin ciki, gama Mai Iko Dukka ya wahalshe ni ƙwarai.


Sa'ad da suka zo Mara, sun kasa shan ruwan Mara saboda ɗacinsa, don haka aka sa masa suna Mara.


Ni Ubangiji na ce sulusi biyu na ƙasar za su hallaka, Sulusi ɗaya ne kawai zai ragu.


Sulusi ɗayan da ya ragu kuwa zan tura cikin wuta, Zan tace su da wuta kamar yadda akan tace azurfa, Zan gwada su kamar yadda akan gwada zinariya. Za su kira gare ni, Zan kuwa amsa musu, Zan ce, ‘Su jama'ata ne,’ Su kuma za su ce, ‘Ubangiji shi ne Allahnmu.’ ”


Sai aka saki mala'ikun nan huɗu, waɗanda aka tanada saboda wannan sa'a, da wannan rana, da wannan wata, da wannan shekara, su kashe sulusin 'yan adam.


Da waɗannan bala'i uku aka kashe sulusin 'yan adam, wato, da wuta, da hayaƙi, da farar wuta da suke fita daga bakinsu.


Wutsiyarsa ta sharo sulusin taurari, ta zuba su a ƙasa. Sai macijin ya tsaya a gaban matar nan mai naƙuda, don ya lanƙwame ɗan nata in ta haife shi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ