Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




W.Yah 15:3 - Littafi Mai Tsarki

3 Suna raira waƙar da Musa bawan Allah ya yi, da kuma wadda ake yi wa Ɗan Ragon nan, suna cewa, “Ayyukanka manya ne, masu banmamaki, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki! Hanyoyinka na adalci ne, na gaskiya ne kuma, Ya Sarkin al'ummai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

3 suka rera waƙar Musa bawan Allah da kuma waƙar Ɗan Ragon suna cewa, “Ayyukanka suna da girma da kuma banmamaki, ya Ubangiji Maɗaukaki. Al’amuranka suna da aminci da kuma gaskiya, ya Sarkin zamanai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




W.Yah 15:3
49 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Abubuwan banmamaki ne Ubangiji yake aikatawa! Duk waɗanda suke murna da su Suna so su fahimce su.


Ina yabonka gama kai abin tsoro ne, Dukan abin da ka yi sabo ne, mai banmamaki. Da zuciya ɗaya na san haka ne.


Ubangiji mai adalci ne a abin da yake yi duka, Mai jinƙai ne a ayyukansa duka.


To, shi Musa mai aminci ne ga dukkan jama'ar Allah a kan shi bara ne, saboda shaida a kan al'amuran da za a yi maganarsu a nan gaba,


Dukan kayayyakin waɗannan jiragen ruwa ba su da amfani, tafiyarsu ba za ta yi nisa ba! Za a kwashe dukan dukiyar sojojin abokan gāba. Za ta yi yawa har sauran jama'a za su sami rabonsu. Ubangiji kansa shi zai zama sarkinmu, zai mallake mu, ya kiyaye mu.


Duk wanda yake da hikima, bari ya fahimci abubuwan nan. Duk wanda yake da ganewa, bari ya san abubuwan nan, Gama hanyoyin Ubangiji masu gaskiya ne, Masu adalci kuwa za su yi tafiya a cikinsu, Amma masu zunubi za su yi tuntuɓe a kansu.


Ki yi murna ƙwarai, ya Sihiyona! Ta da murya ya Urushalima! Ga Sarkinki yana zuwa wurinki, Shi mai adalci ne, mai nasara, Shi kuma mai tawali'u ne, Yana bisa kan jaki, a kan aholaki.


Domin Shari'a, ta hannun Musa aka ba da ita, alheri da gaskiya kuwa ta wurin Yesu Almasihu suka kasance.


Ubangiji nagari ne, Ƙaunarsa madawwamiya ce, Amincinsa kuwa har abada abadin ne.


A lokacin da Abram yake da shekara tasa'in da tara Ubangiji ya bayyana gare shi, ya ce masa, “Ni ne Allah Mai Iko Dukka. Ka yi mini biyayya, ka zama kamili.


Don hukuncinsa daidai yake, na adalci ne, Ya hukunta babbar karuwar nan wadda ta ɓata duniya da fasikancinta, Ya kuma ɗauki fansar jinin bayinsa a kanta.”


Suna raira wata sabuwar waƙa a gaban kursiyin, a gaban rayayyun halittan nan huɗu, da kuma a gaban dattawan nan. Ba mai iya koyon waƙar nan, sai mutum dubu ɗari da dubu arba'in da huɗu ɗin nan, waɗanda aka fanso daga duniya.


Sa'an nan Musa ya hurta kalmomin wannan waƙa a kunnen dukan taron jama'ar Isra'ila har ƙarshensu.


Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, Ɗan Ragon kuwa zai cinye su, shi da waɗanda suke tare da shi, kirayayyu, zaɓaɓɓu, amintattu, domin shi ne Ubangijin iyayengiji.”


Suna cewa, “Mun gode maka, ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, Wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, Saboda ka ɗauki ikonka mai girma, kana mulki.


Su rayayyun halittan nan huɗu kuwa, kowaccensu tana da fikafikai shida, jikinsu duk idanu ne ciki da waje, dare da rana kuwa ba sa daina waƙa, suna cewa, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki, Ubangiji Allah Maɗaukaki, Shi ne a dā, shi ne a yanzu, shi ne kuma a nan gaba!”


Da ya zo kusa da kogon da Daniyel yake, sai ya ta da murya ya yi kira da damuwa, ya ce wa Daniyel, “Ya Daniyel, bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta masa kullum, yana da ikon cetonka daga zakoki?”


Ku zo ku gabatar da matsalarku a ɗakin shari'a, Bari waɗanda aka kai ƙara su yi shawara da juna. Wane ne ya faɗi abin da zai faru, Ya kuma yi annabci tuntuni? Ashe, ba ni ba ne, Ubangiji, Allah wanda ya ceci mutanensa? Ba wani Allah sai ni.


Mutane za su yi magana a kan manya manyan ayyukanka, Ni kuwa zan yi shelar girmanka.


Maɗaukaki kana ƙaunar abin da yake daidai, Ka kawo adalci cikin Isra'ila, Ka kawo adalci da gaskiya.


Da wani suna a rubuce a jikin rigarsa, har daidai cinyarsa, wato Sarkin sarakuna, Ubangijin iyayengiji.


Ubangiji wanda yake cikinsa mai adalci ne, Ba ya kuskure. Yakan nuna adalcinsa kowace safiya, Kowace safiya kuwa bai taɓa fāsawa ba. Amma mugu bai san kunya ba.


Za ka nuna wa Yakubu aminci, Ga Ibrahim kuma madawwamiyar ƙauna, Kamar yadda ka rantse wa kakanninmu Tun a zamanin dā.


Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim, Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu, Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki, Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.


Kakanninsu na kallo sa'ad da Allah ya aikata wata mu'ujiza A filin Zowan a ƙasar Masar.


Ba za mu iya fahimtar manyan abubuwa da yake yi ba, Al'ajabansa kuwa ba su da iyaka.


Sai sarki ya kira Yehoyada babban firist, ya ce masa, “Don me ba ka sa Lawiyawa su tafi Yahuza, da Urushalima, su karɓo kuɗin da Musa, bawan Ubangiji, ya aza wa taron jama'ar Isra'ila su kawo domin alfarwar sujada ba?”


Amma Haruna da 'ya'yansa maza suka miƙa hadayu a kan bagaden hadaya ta ƙonawa, da kan bagaden ƙona turare, domin dukan aikin Wuri Mafi Tsarki, da kuma yin kafara domin Isra'ila bisa ga dukan abin da Musa, bawan Allah, ya umarta.


Sai kuma mala'ika na biyu ya biyo, yana cewa, “Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi! Ita da ta zuga dukkan al'ummai su yi tsananin jarabar yin fasikanci da ita.”


Dukan Isra'ilawa sun karya dokokinka, sun kauce, sun ƙi bin maganarka. La'ana da rantsuwa waɗanda suke a rubuce cikin dokokin Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi.


Ka koya musu su kiyaye Asabar ɗinka tsattsarka, Ka kuma ba su dokokinka ta hannun Musa bawanka.


Nan fa, a ƙasar Mowab, Musa bawan Ubangiji, ya rasu kamar yadda Ubangiji ya faɗa.


Gama zan yi shelar sunan Ubangiji, In yabi girman Allahnmu!


Sai dai ku kiyaye umarnai da dokokin da Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin tafarkunsa, ku kiyaye dokokinsa, ku manne masa, ku bauta masa da zuciya ɗaya da dukan ranku.”


“Ka tuna ka girmama aikinsa, Wanda mutane suke yabo.


Wannan Allah dai! Ayyukansa kamiltattu ne ƙwarai, Maganarsa abar dogara ce! Kamar garkuwa yake, ga duk mai neman taimako a wurinsa.


Ayyukanka da girma suke, ya Ubangiji! Tunaninka da zurfi suke!


Iyakar abin da yake yi duka, da aminci da adalci ne. Dukan umarnansa, abin dogara ne.


Girma da ɗaukaka su tabbata ga Sarkin zamanai, marar mutuwa, marar ganuwa, Allah Makaɗaici, har abada abadin. Amin, amin.


“Ni ne Alfa. Ni ne Omega,” in ji Ubangiji Allah, wanda yake a yanzu, shi ne a dā, shi ne kuma a nan gaba, Maɗaukaki.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ