Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Waƙar Waƙoƙi 5:16 - Littafi Mai Tsarki

16 Bakinsa yana da daɗin sumbata, Kome nasa yana faranta mini rai. Matan Urushalima, yadda ƙaunataccena yake ke nan.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

16 Bakinsa zaƙi ne kansa; komensa yana da kyau. Haka ƙaunataccena, abokina, yake ’yan matan Urushalima.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Waƙar Waƙoƙi 5:16
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kai ne mafi kyau a cikin dukan mutane, Kai mai kyakkyawan lafazi ne, Kullum Allah yakan sa maka albarka!


Bakinki kamar ruwan inabi mafi kyau ne. Idan haka ne bari ya bulbulo sosai zuwa ga ƙaunataccena, Ya gangara leɓunan masu barci.


Maciya amana! Ashe, ba ku sani abuta da duniya gāba ce da Allah ba? Saboda haka, duk mai son abuta da duniya, yā mai da kansa mai gāba da Allah ke nan.


Aka kuma cika Nassin nan da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, bangaskiyar nan tasa kuma aka lasafta ta adalci ce a gare shi,” aka kuma kira shi aminin Allah.


Dahir na ɗauki dukkan abubuwa hasara ne, a kan mafificiyar darajar sanin da nake yi na Almasihu Yesu Ubangijina. Saboda shi ne na zaɓi yin hasarar dukkan abubuwa, har ma na mai da su tozari domin Almasihu yă zama nawa,


An gicciye ni tare da Almasihu. Yanzu ba ni ne kuma nake a raye ba, Almasihu ne yake a raye a cikina. Rayuwar nan kuma da nake yi ta jiki, rayuwa ce ta wurin bangaskiya ga Ɗan Allah, wanda ya ƙaunace ni, har ya ba da kansa domina.


Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka sāke tafiya, ka ƙaunaci karuwa wadda take tare da kwartonta. Ka ƙaunace ta kamar yadda ni Ubangiji nake ƙaunar mutanen Isra'ila, ko da yake suna bin gumaka, suna ƙaunar wainar zabibi da aka miƙa wa gumaka.”


Maganarka da na samu na ci. Maganarka kuwa ta zama abar murna a gare ni, Ta faranta mini zuciya. Gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Mai Runduna.


Hakika kamar yadda mace marar aminci takan bar mijinta, Haka kun zama marar aminci a gare ni, ya jama'ar Isra'ila. Ni Ubangiji, na faɗa.”


Ƙaunataccena nawa ne, ni kuma tasa ce, Yana kiwon garkensa a cikin bi-rana.


Ƙaunataccena nawa ne, ni ma tasa ce, Yana kiwon garkensa a cikin furannin bi-rana,


Kamar yadda itacen gawasa yake a cikin itatuwan jeji, Haka ƙaunataccena yake a cikin sauran maza. Da farin ciki na zauna a inuwarsa, Ina jin daɗin halinsa ƙwarai.


Ni fure ce na Sharon, Furen bi-rana na cikin kwari.


Kai kyakkyawa ne ƙwarai, ya ƙaunataccena, kana da bansha'awa. Koriyar ciyawa ita ce gadonmu.


Leɓunanka sun lulluɓe ni da sumba, Ƙaunarka ta fi ruwan inabi zaƙi.


Bari dukansu su yabi sunan Ubangiji, Sunansa ya fi dukan sauran sunaye girma, Ɗaukakarsa kuwa tana bisa duniya da samaniya!


Ɗanɗanon ka'idodinka akwai zaƙi, Har sun fi zuma zaƙi!


Ba wani kamarka a Sama, ya Ubangiji, Ba wani daga su cikin talikai da yake daidai da kai.


Abin da ake so ne fiye da zinariya, I, fiye da tatacciyar zinariya ma, Sun fi zuma zaƙi, I, fiye da tatacciyar zuma ma.


“Saul da Jonatan ƙaunatattu ne, suna da bansha'awa, A raye suna tare, haka kuma a mace suna tare. Sun fi gaggafa sauri, Sun fi zaki ƙarfi.


Rana ta sa na zama akawala kyakkyawa. Matan Urushalima, bisa ga launi, ni ƙasa ƙasa ce, Kamar alfarwar hamada, Kamar labulen fādar Sulemanu.


Leɓunanki ja wur kamar kin shafa jan-baki. Maganarki tana faranta zuciya. Kumatunki suna haske bayan lulluɓi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ