Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Romawa 15:26 - Littafi Mai Tsarki

26 Mutanen Makidoniya da na Akaya, sun ji daɗin yin gudunmawar daidai gwargwado ga matalauta, a cikin tsarkakan da suke a Urushalima.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

26 Gama Makidoniya da Akayya sun ji daɗin yin gudummawa domin matalautan da suke cikin tsarkakan da suke a Urushalima.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Romawa 15:26
33 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Domin aikin nan na alheri, ba biyan bukatar tsarkaka kaɗai yake yi ba, har ma yana ƙara yawaita godiya ga Allah ƙwarai da gaske.


domin na san niyyarku, har ma ina taƙama da ku gun mutanen Makidoniya a kan haka, ina ce musu Ikkilisiyar Akaya ta yi shiri tun bara, ƙwazonku kuwa ya ta da yawancinsu.


saboda nakan ji labarin ƙauna da bangaskiya da kake yi wa Ubangiji Yesu da dukkan tsarkaka.


To, 'yan'uwa, kun sani fa jama'ar gidan Istifanas su ne nunan fari a ƙasar Akaya, sun kuwa ba da kansu ga yi wa tsarkaka hidima.


Amma sa'ad da Galiyo yake muƙaddashin ƙasar Akaya, Yahudawa suka tasar wa Bulus da nufi ɗaya suka kawo shi a gaban shari'a,


Wata rana da daddare aka yi wa Bulus wahayi, ya ga wani mutumin ƙasar Makidoniya na tsaye, yana roƙonsa yana cewa, “Ka ƙetaro Makidoniya, ka taimake mu mana.”


Amma in za ka kira biki, sai ka gayyayo gajiyayyu, da musakai, da guragu, da makafi,


Sai ya ɗaga kai, ya dubi almajiransa, ya ce, “Albarka tā tabbata gare ku, ku matalauta, domin Mulkin Allah naku ne.


Kullum kuna tare da talakawa, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba.


Sai Sarkin zai amsa musu ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, tun da yake kun yi wa ɗaya daga cikin waɗannan 'yan'uwana mafi ƙanƙanta, ai, ni kuka yi wa.’


Da haka aka karya alkawarina a wannan rana. Masu tumakin kore suna tsaye suna kallon abin da na yi, sai suka gane lalle wannan maganar Ubangiji ce.


Sai na zama makiyayi na masu tumakin kore. Na kuwa ɗauko sanda biyu, na ce da ɗaya “Alheri,” ɗaya kuma na ce da shi “Haɗa Kai.” Sai na yi kiwon tumakin.


Wanda ya yi wa matalauci ba'a, Mahaliccinsa yake yi wa zargi. Idan kana murna da hasarar wani, za a hukunta ka.


Wanda ya zalunci matalauci ya zargi Mahaliccinsa ke nan, amma nuna alheri ga matalauci yin sujada ne.


Idan kana so ka zama mai farin ciki, sai ka nuna alheri ga matalauci. Zunubi ne ka raina kowane mutum.


Amma Hananiya ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, na sha jin labarin mutumin nan gun mutane da yawa, kan yawan muguntar da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.


daga nan kuma sai Filibi ta ƙasar Makidoniya, wadda take babbar alkarya ce a wannan waje, birnin Romawa ne kuma. A nan birnin muka yi 'yan kwanaki.


Bayan waɗannan al'amura Bulus ya ƙudura a ransa, cewa in ya zazzaga ƙasar Makidoniya da ta Akaya, za shi Urushalima, ya kuma ce, “Bayan na je can, lalle ne kuma in je in ga birnin Roma.”


Zan zo gare ku bayan na zazzaga ƙasar Makidoniya, don kuwa ta Makidoniya zan bi.


Wato niyyata in bi a kanku in za ni Makidoniya, in kuma komo wurinku daga Makidoniya, sa'an nan ku yi mini rakiya in zan tafi Yahudiya.


duk da haka dai hankalina bai kwanta ba, domin ban tarar da ɗan'uwana Titus a can ba, saboda haka, sai na yi bankwana da su, na zarce na tafi Makidoniya.


Ko a lokacin da muka zo ƙasar Makidoniya ma, ba mu sami shaƙatawa ba, ana ta wahalshe mu ta kowace hanya, a waje ga husuma, a zukatanmu kuma ga fargaba.


Don kada ya zamana in waɗansu mutanen Makidoniya sun zo tare da ni, suka tarar ba ku shirya ba, kunya ta ishe mu, balle fa ku, saboda amincewa da muke yi da ku.


Sa'ad da nake a wurinku kuma nake zaman rashi, ban nauyaya wa kowa ba, domin 'yan'uwan da suka zo daga Makidoniya su ne suka biya mini bukata. Saboda haka, na ƙi nauyaya muku ta kowace hanya, ba kuwa zan nauyaya muku ba.


Ku kuma Filibiyawa, ku kanku kun sani tun da aka fara yin bishara, sa'ad da na bar ƙasar Makidoniya, ba wata ikkilisiyar da ta yi tarayya da ni wajen hidimar bayarwa da karɓa, sai dai ku kaɗai.


Ku ma har kuka zama abin koyi ga dukan masu ba da gaskiya a ƙasar Makidoniya da ta Akaya.


Domin daga gare ku ne aka baza Maganar Ubangiji, ba ma a ƙasar Makidoniya da ta Akaya kaɗai ba, har ma a ko'ina bangaskiyarku ga Allah ta shahara, har ma ya zamana, ba sai lalle mun faɗa ba.


Hakika kuwa kuna ƙaunar dukan 'yan'uwa a duk ƙasar Makidoniya. Sai dai muna muku gargaɗi, 'yan'uwa, ku ƙara yin haka ƙwarai da gaske,


Kamar yadda na roƙe ka, ka dakata a Afisa sa'ad da za ni ƙasar Makidoniya, ka gargaɗi waɗansu mutane kada su koyar da wata koyarwa dabam,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ