Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Romawa 11:1 - Littafi Mai Tsarki

1 To, ina tambaya. Wato, Allah ya juya wa jama'arsa baya ke nan? A'a, ko kusa! Ai, ni ma da kaina Ba'isra'ile ne, zuriyar Ibrahim, na kabilar Biliyaminu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Romawa 11:1
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

In su Ibraniyawa ne, ni ma haka. In su Isra'ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka.


Gama Ubangiji ya yi ƙaƙƙarfan alkawari, ba zai yashe ku ba, gama ya ɗauri aniya ya maishe ku jama'arsa.


An yi mini kaciya a rana ta takwas, asalina Isra'ila ne, na kabilar Biliyaminu, Ba'ibrane ɗan Ibraniyawa, bisa ga Shari'a kuwa ni Bafarisiye ne,


“Irin zaman da na yi tun daga ƙuruciyata, wato tun da farko, a cikin jama'armu da kuma a Urushalima har ya zuwa yau, sananne ne ga dukan Yahudawa.


“Ni bayahude ne, haifaffen Tarsus, ƙasar Kilikiya, amma a nan garin na girma, aka kuma karantar da ni wurin Gamaliyal, bisa ga tsarin tsanantacciyar hanyar nan ta Shari'ar kakanninmu. Ina mai himmar bauta wa Allah, kamar yadda dukanku kuke a yau,


Allahna zai ƙi su Domin ba su yi masa biyayya ba. Za su zama masu yawo cikin al'ummai.


Ubangiji ba zai rabu da jama'arsa ba, Ba zai rabu da waɗanda suke nasa ba.


Da ma a la'ance ni, a raba ni da Almasihu saboda dangina, 'yan'uwana na kabila!


A'a, ko kusa! A dai tabbata Allah mai gaskiya ne, ko da yake kowane mutum maƙaryaci ne, yadda yake a rubuce cewa, “Don maganarka tă tabbatar da adalcinka, Ka kuma yi rinjaye in an binciki al'amarinka.”


Ubangiji kuwa ya ce, “Zan kawar da jama'ar Yahuza daga gabana kamar yadda na kawar da jama'ar Isra'ila. Zan yi watsi da birnin nan da na zaɓa, wato Urushalima, da Haikalin da na ce sunana zai kasance a wurin.”


A kullum ne Ubangiji zai yashe ni? Ba kuma zai ƙara yin murna da ni ba?


Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar.” Da suka ji haka, suka ce, “Allah ya sawwaƙe!”


Ina kuma tambaya. Faɗuwar da suka yi, sun faɗi ba tashi ke nan? A'a, ko kusa! Sai ma faɗuwarsu ta zama sanadin ceto ga al'ummai, don a sa Isra'ila kishi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ