Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Obadiya 1:19 - Littafi Mai Tsarki

19 Isra'ilawan da yake Negeb za su mallaki dutsen Isuwa, Waɗanda suke a filaye na Yahuza za su mallaki ƙasar Filistiya. Isra'ilawa za su mallaki yankin ƙasar Ifraimu da Samariya, Jama'ar Biliyaminu za su mallaki Gileyad.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

19 Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Obadiya 1:19
33 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ta haka jama'ar Isra'ila za ta ci nasara bisa sauran ƙasar Edom wadda ta ragu, Da bisa dukan al'umman da a dā su nawa ne,” In ji Ubangiji, wanda zai sa al'amarin ya auku.


Za a sayi gonaki da kuɗi, a sa hannu a kan sharuɗa, a hatimce su a gaban shaidu, a ƙasar Biliyaminu da wuraren da suke kewaye da Urushalima, da cikin garuruwan Yahuza, da na garuruwan ƙasar tudu, da a garuruwan kwaruruka, da a garuruwan Negeb, gama zan komar wa mutane da wadatarsu a ƙasarsu, ni Ubangiji na faɗa.”


Za ku zauna cikin ƙasar da na ba kakanninku. Za ku zama mutanena, ni kuma in zama Allahnku.


Sai ka yi kiwon mutanenka da sandanka, Wato garken mallakarka, Wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi A tsakiyar ƙasa mai albarka. Bari su yi kiwo cikin Bashan da Gileyad Kamar a kwanakin dā.


Ubangiji ya ce, “Mutanen Ammon sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don haɗamarsu ta ƙasa, Suka tsaga mata masu ciki a Gileyad.


Zan kawar da masu sarautar biranen Ashdod da Ashkelon, Zan karɓe sandan mulkin Ekron. Sauran Filistiyawa da suka ragu kuma, Za su mutu duka.”


domin haka ni Ubangiji Allah zan hukunta Filistiyawa. Zan kashe Keretiyawa, in hallaka sauran mazaunan gāɓar teku.


Wannan shi ne abin da Ubangiji ya faɗa akan Ammonawa, “Isra'ila ba shi da 'ya'ya ne? Ko kuwa ba shi da māgada ne? Me ya sa waɗanda suke bautar Milkom suka mallaki inda Gad take zama, Suka zauna a garuruwanta?


Gama zai ceci Sihiyona, Ya sāke gina garuruwan Yahuza, Jama'arsa za su zauna a wurin, su mallaki ƙasar.


Sarki kuma ya aika musu da amsa ya ce, “Gaisuwa zuwa ga Rehum shugaban sojoji, da Shimshai magatakarda, da abokansu waɗanda suke zaune a Samariya da lardin Yammacin Kogi.


sai suka tafi wurin Zarubabel, da shugabannin gidajen kakanni, suka ce musu, “Ku yarda mana mu yi ginin tare, gama muna yi wa Allahnku sujada kamar yadda kuke yi, muna kuma ta miƙa masa sadaka tun kwanakin Esar-haddon, Sarkin Assuriya, wanda ya kawo mu nan.”


Don haka Allah na Isra'ila ya zuga Ful, Sarkin Assuriya, wato Tiglat-filesar, ya zo ya kwashe su, ya kai su bauta, wato su Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa. Ya kai su Hala, da Habor, da Hara, har zuwa kogin Gozan, can suke har yau.


Sarkin Assuriya kuwa ya kawo mutane daga Babila, da Kuta, da Awwa, da Hamat, da Sefarwayim, ya zaunar da su a garuruwan Samariya a maimakon jama'ar Isra'ila. Sai suka mallaki Samariya, suka zauna a garuruwanta.


Na filayen kwarin kuwa, su ne Eshtawol, da Zora, da Ashna,


Biranen jama'ar Yahuza da suke can kudu sosai wajen iyakar Edom, su ne Kabzeyel, da Eder, da Yagur,


da rabin Gileyad, da Ashtarot, da Edirai, wato garuruwan sarki Og a Bashan. Mutanen Makir ne, ɗan Manassa, aka ba su wannan bisa ga iyalansu.


Yankin ƙasarsu shi ne Yazar, da dukan biranen Gileyad da rabin ƙasar Ammonawa zuwa Arower wadda take gabas da Rabba,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ