Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Nehemiya 8:12 - Littafi Mai Tsarki

12 Sai jama'a duka suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci. Suka yi murna ƙwarai domin sun fahimta dokokin da aka karanta musu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

12 Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Nehemiya 8:12
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ina sa zuciya ga cetonka ƙwarai, ya Ubangiji! Ina samun farin ciki ga dokarka.


Suka ce wa juna, “Ashe, zuciyarmu ba ta yi annuri ba, sa'ad da yake a hanya, yana bayyana mana Littattafai?”


Zan yabe ka kullayaumin Domin ka koya mini ka'idodinka.


Fassarar koyarwarka takan ba da haske, Takan ba da hikima ga wanda bai ƙware ba.


Ina ƙaunar umarnanka, fiye da zinariya, Fiye da zinariya tsantsa.


Umarnanka nawa ne har abada, Su ne murnar zuciyata.


Ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina ta tunani a kanta dukan yini.


Dokar da ka yi Muhimmiya ce a gare ni, Fiye da dukan dukiyar duniya.


Ina murna da dokokinka, Ba zan manta da umarnanka ba.


Ina murna da bin umarnanka, Fiye da samun dukiya mai yawa.


A kullum ina aikata abin da Allah ya umarta, Ina bin nufinsa, ba nufin kaina ba.


Don na sani ba wani abin kirki da ya zaune mini, wato a jikina. Niyyar yin abin da yake daidai kam, ina da ita, sai dai ikon zartarwar ne babu.


Maganarka da na samu na ci. Maganarka kuwa ta zama abar murna a gare ni, Ta faranta mini zuciya. Gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Mai Runduna.


Mazaunan duniya kuma, sai su yi ta alwashi a kansu, suna ta shagali, suna a'aika wa juna da kyauta, domin annabawan nan biyu dā sun azabtar da mazaunan duniya.


Sa'an nan ya ce musu, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha ruwan inabi mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi, gama wannan rana tsattsarka ce ta Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin da Ubangiji ya ba ku shi ne ƙarfinku.”


Lawiyawa kuma suka bi suna rarrashin jama'a, suna cewa, “Ku yi shiru, gama wannan rana tsattsarka ce, kada ku yi baƙin ciki.”


Kashegari kuma sai shugabannin kakannin gidajen jama'a duka, tare da firistoci, da Lawiyawa, suka je wurin Ezra, magatakarda, domin su yi nazarin dokokin.


Su ne ranakun da Yahudawa suka sami kuɓuta daga abokan gābansu. A wannan wata ne kuma baƙin cikinsu ya zama farin ciki, makokinsu kuma ya zama hutawa. Sai su maishe su ranakun biki da farin ciki, da aika wa juna da abinci, da kuma ba da kyautai ga matalauta.


Sai suka ci, suka sha, suka yi murna a gaban Ubangiji a wannan rana. Sai suka sake shelar naɗin Sulemanu ɗan Dawuda sarki, a karo na biyu, suka shafa masa man keɓewa domin ya zama mai mulki na Ubangiji, Zadok kuwa shi ne firist.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ