Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Nehemiya 2:20 - Littafi Mai Tsarki

20 Ni kuwa sai na amsa musu, na ce, “Allah na Sama zai ba mu nasara, saboda haka mu mutanensa za mu tashe, mu kama gini, amma ba ruwanku, ba hakkinku, ba ku da wani abin tunawa a Urushalima.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

20 Na amsa musu na ce, “Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa za mu tashi mu fara gini, amma game da ku kam, ba ku da rabo cikin Urushalima, ba ku da wani hakki ko wani abin tunawa.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Nehemiya 2:20
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ba ruwanka da wannan al'amari sam, don zuciyarka ba ɗaya take ba a gaban Allah.


Amma Zarubabel, da Yeshuwa, da shugabannin gidajen kakannin Isra'ila suka ce musu, “Ba abin da za ku yi tare da mu na ginin Haikalin Allahnmu, amma mu kaɗai za mu yi wa Ubangiji Allah na Isra'ila, gini kamar yadda sarki Sairus, wato Sarkin Farisa, ya umarce mu.”


Sa'an nan sarki ya ce mini, “To, me kake so?” Sai na yi addu'a ga Allah na Sama,


ya ce, ‘Ya Karniliyas, an amsa addu'arka sadakarka kuma ta zama abar tunawa ga Allah.


Ka sa waɗanda suke murna da kuɓutata Su yi ta sowa ta murna, suna cewa, “Ubangiji mai girma ne! Yana murna da cin nasarar bawansa!”


zan ba ku matuni da suna a Haikalina da cikin garukana, da sun fi na 'ya'ya mata da maza. Zan ba ku tabbataccen suna wanda ba za a raba ku da shi ba.”


Idan ka riƙe wannan zai amfane ka. Kada ka bar wancan, gama shi wanda yake tsoron Allah zai yi amfani da su.


Ya Allah, ka yi wa Sihiyona alheri, ka taimake ta, Ka sāke gina garun Urushalima.


Mu kuma, sai mu yi sowa ta farin ciki saboda ka ci nasara, Mu yi bikin cin nasara da ka yi, Da yabon Ubangiji Allahnmu. Allah ya amsa dukan roƙe-roƙenka!


Shi kuwa ya zura masa ido a tsorace, ya ce, “Ya Ubangiji, mene ne?” Mala'ikan kuma ya ce masa, “Addu'arka da sadakarka sun kai har a gaban Allah, abubuwan tunawa ne kuma a gare shi.


Kambin zai kasance a Haikalin Ubangiji don tunawa da Heldai, da Tobiya, da Yedaiya, da Yosiya ɗan Zafaniya.


Ku yi wa Urushalima addu'ar salama! “Allah ya sa masu ƙaunarki su arzuta!


“Dukan barorin sarki da mutanen lardunan sarki sun sani duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, ba tare da an kira shi ba, to, doka ɗaya ce take kan mutum, wato kisa, ko mace ko namiji, sai dai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don ya rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.”


Ya mai da hankalinsa ga bin Ubangiji a kwanakin Zakariya, wanda ya koya masa tsoron Allah. Dukan lokacin da yake bin Ubangiji, Allah ya wadata shi.


A ranar murnarku, da lokacin ƙayyadaddun idodinku, da tsayawar watanninku, za ku busa kakakin a lokacin yin hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama. Za su zama sanadin tunawa da ku a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”


Duk sa'ad da Haruna zai shiga Wuri Mai Tsarki, zai ɗauki sunayen 'ya'yan Isra'ila a gaban Ubangiji kullum, a kan ƙyallen maƙalawa domin nemar musu nufin Allah.


Sai a sa lubban tsantsa a kowane jeri don a haɗa da abincin da za a ƙone domin hadaya ta tunawa ga Ubangiji.


Zai kuma kawo hadayarsa a wurin 'ya'yan Haruna maza, firistoci. Zai ɗibi tāfi guda na lallausan garin da aka zuba wa mai da dukan lubban. Firist kuwa zai ƙona wannan a kan bagaden don tunawa, gama hadaya ta ƙonawa ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.


Da na ji wannan labari, sai na zauna, na yi kuka. Na yi kwanaki ina baƙin ciki, na yi ta azumi da addu'a a gaban Allah na Sama.


Zai saurari jama'arsa wadda ya rabu da ita, Zai kuwa ji addu'arta.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ