Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Nehemiya 2:17 - Littafi Mai Tsarki

17 Sa'an nan na ce musu, “Kun ga irin wahalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta. Ku zo, mu sāke gina garun Urushalima don mu fita kunya.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

17 Sai na ce musu, “Kun ga matsalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sāke gina katangar Urushalima, ba za mu ƙara shan kunya ba.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Nehemiya 2:17
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zan kuma maishe ki kufai da abin zargi ga al'ummai da suke kewaye da ke, da kuma a idanun dukan masu wucewa.


Sai suka ce mini, “Waɗanda suka tsira, suka koma daga zaman talala, da suke can lardin, suna cikin wahala ƙwarai, suna kuma shan kunya. Garun Urushalima kuma ya rushe, ƙofofi sun ƙone.”


Sauran al'ummar da take kewaye da mu, Suka maishe mu abin ba'a, suka yi mana dariya, Suka yi mana ba'a.


Ganin azabar 'yan matan birnina Ya sa ni baƙin ciki.


Dukan wuraren zaman Yakubu, Ubangiji ya hallakar ba tausayi, Da fushinsa kuma ya rurrushe kagaran Sihiyona. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulkin.


Zan maishe su abin ƙyama da masifa ga mulkokin duniya duka. Za su zama abin zargi, da karin magana, da ba'a, da la'ana a dukan wuraren da zan warwatsa su.


Ya Ubangiji, ka rama wa al'umman nan har sau bakwai, Saboda tsiwace-tsiwacen da suka yi maka.


Maƙwabtanmu suna yi mana dariya saboda kai, Suna yi mana ba'a, sun maishe mu abin wasa.


Nahash Ba'ammone kuwa ya ce, “Zan ƙulla amana da ku a kan wannan sharaɗi, wato in ƙwaƙule idanunku na dama don ku zama abin raini ga Isra'ilawa.”


Da na fita, sai na bi ta Ƙofar Kwari zuwa Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, na dudduba garun Urushalima, wanda aka rushe, da ƙofofinsa da wuta ta cinye.


Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da na yi ba, gama ban riga na faɗa wa Yahudawa, da firistoci, da manyan gari, da shugabanni, da sauran waɗanda za su yi aikin ba.


Sai Shallum ɗan Kolhoze, mai mulkin yankin Mizfa ya gyara Ƙofar Maɓuɓɓuga, ya gina ta, ya rufe ta, ya sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta. Ya kuma gina garun Tafkin Siluwam na gonar sarki, har zuwa matakan da suka gangaro daga Birnin Dawuda.


Gama mu bayi ne, duk da haka Allahnmu bai manta da mu a bautarmu ba, amma ya sa muka sami tagomashi a wurin sarakunan Farisa, suka iza mu domin mu gina Haikalin Allahnmu, mu sāke gyaransa, mu kuma gina garu a Yahuza da Urushalima.


Ka maishe mu abin raini a wurin arna, Suna kaɗa mana kai, suna raina mu.


Sauran al'umma za su ji tsoron Ubangiji, Dukan sarakunan duniya za su ji tsoron ikonsa.


Za a faɗaɗa iyakarka A ranar da za a gina garunka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ