Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Nahum 2:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Nineba tana kama da tafki wanda ruwansa yake zurarewa, Suna cewa, “Tsaya, tsaya,” Amma ba wanda ya waiga.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Nahum 2:8
15 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sai mala'ikan nan ya ce mini, “Ruwan nan da ka gani, a inda karuwar nan take a zaune, jama'a ce iri iri, da taro masu yawa, da al'ummai, da harsuna.


Sai ɗaya daga cikin mala'ikun nan bakwai masu tasoshin nan bakwai, ya zo ya yi mini magana, ya ce, “Zo in nuna maka hukuncin da za a yi wa babbar karuwar nan, wadda take zaune a bisa ruwa mai yawa,


Shugabanninki kamar ɗango suke, Manyan mutanenki kamar cincirindon fāra ne, Suna zaune a kan shinge a kwanakin sanyi, Sa'ad da rana ta fito, sukan tashi su tafi, Ba wanda ya san inda suke.


Sojojin Babila sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata, An sa wa wuraren zamanta wuta, An karya ƙyamaren ƙofofin garinta.


Ku datse wa Babila mai shuka, Da mai yanka da lauje a lokacin girbi. Saboda takobin azzalumi, Kowa zai koma wurin mutanensa, Kowa kuma zai gudu zuwa ƙasarsa.”


Ubangiji ya yi tambaya ya ce, “Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, An ci sojojinsu, suna gudu, Ba su waiwayen baya, akwai tsoro a kowane sashi.”


Ku fita daga Babila, ku tafi a sake! Ku yi sowar albishir da farin ciki, ku sa a sani a ko'ina, “Ubangiji ya fanshi bawansa Isra'ila!”


Kome shawarar da kika samu ba ki da ƙarfi. Bari mashawartanki su fito su cece ki, Waɗancan mutane masu binciken taurari Waɗanda suka zana taswirar sammai, Su kuma faɗa miki Dukan abin da zai faru da yake wata wata.


“Baƙin da yake zaune a Babila za su gudu zuwa ƙasashensu, suna a warwatse kamar bareyin da suke tsere wa maharbansu, kamar tumakin da ba su da makiyayi.


Daga wannan ƙasa ya tafi Assuriya ya gina Nineba da Rehobot-ir, da Kala,


Ƙarshenki ya zo, Ke mai zama kusa da ruwa mai yawa, Mai yawan dukiya. Ajalinki ya auka.


Da jin takawar kofatan dawakai, Da amon karusai da ƙafafun karusai, Ubanni ba su juya, su dubi 'ya'yansu ba, Domin hannuwansu sun yi laƙwas,


Jawabi a kan Nineba ke nan, a littafin wahayin Nahum na Elkosh.


Muryata ƙarama ce, ba kuma ƙarfi, Na kuwa yi kuka kamar kurciya, Idanuna sun gaji saboda duban sama. Ya Ubangiji, ka cece ni daga dukan wannan wahala.


Dukanmu muna gurnani kamar beyar, muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci, amma ina. Muna ta neman ceto, amma ya yi nisa da mu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ